Shirin Zanga Zanga a Kano: 'Yan Sanda sun Mika Bukatunsu ga Matasa

Shirin Zanga Zanga a Kano: 'Yan Sanda sun Mika Bukatunsu ga Matasa

  • Dukkanin masu ruwa da tsaki, musamman hukumomin tsaron Najeriya sun fara daura damarar tunkarar zanga-zanga da ake shirin yi
  • Rundunar 'yan sanda a Kano ta gudanar da muhimmin taro da sauran shugabannin hukumomin tsaro a jihar domin hana ayyukan miyagu
  • Daga cikin shugabannin da aka zauna da su akwai sojoji da hukumar tsaron fararen hula da bijilanti da hukumar hana fasa kwauri

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano - Rundunar 'yan sandan Kano ta bayyana cewa yayin da wasu matasa ke shirin shiga zanga-zanga, su ma sun shirya tunkarar lamarin a mako mai zuwa.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: 'Yan kasuwa a Kano sun dauki matakin tsare dukiyoyinsu

Jami'in hulda da rundunar na Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyana cewa sun zauna da sauran shugabannin hukumomin tsaro domin fitar da hanyar da za a tarbi zanga-zanga a jihar.

Yan sanda
Zanga-zanga: Hadakar hukumomin tsaro sun shirya bayar da kariya a Kano Hoto: Abdullahi Haruna Kiyawa
Asali: Facebook

A sanarwar da ya wallafa a shafinsa na Facebook, SP Kiyawa ya bayyana cewa sun fitar da matakai da dama da za su taimaka wajen gudanar da zanga-zanga a cikin lumana.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wasu matakai aka dauka kan Zanga-zanga?

Rundunar yan sandan Kano ta ce za ta yi aiki da sauran jami'ai wajen dakile yunkurin masu shirin tayar da hankula a lokutan zanga zanga.

Radio Nigeria ta wallafa cewa yan sandan na cikin shirin kar-ta-kwana domin tabbatar da ba a salwantar da rayuka ba idan an fara zanga zanga.

Zanga-zanga: Yan sanda sun mika bukatunsu

Rundunar yan sanda ta mika jerin bukatunta ga masu shirin shiga zanga-zangar gama gari da za a fara daga 1-10 Agusta, 2024.

Kara karanta wannan

Rundunar 'yan sanda ta gano manyan matsalolin da zanga zanga za ta iya haifarwa

Jami'in hulda da jama'a na rundunar ya lissafa bukatunsu da suka hada da ba su bayanan a kan hanyoyin da za a bi, lokacin da za a fara da kuma kammala da sunayen jagororin zanga-zangar.

Kwankwaso ya fadi mafita a madadin zanga-zanga

A baya kun ji cewa tsohon dan takarar shugaban kasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bayar da mafita da za ta fi alheri ga 'yan kasar nan a maimakon tsunduma zanga-zanga.

Sanata Kwankwaso ya bayyana cewa kamata ya yi jama'a su tanadi katunan zabensu domin kawar da gwamnatin Bola Tinubu a kakar zabe mai zuwa tun da ta gaza tafiyar da kasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.