Abubuwa 7 da Suka Jawowa Gwamnatin Tinubu Zanga Zanga Shekara 1 da Hawa Mulki

Abubuwa 7 da Suka Jawowa Gwamnatin Tinubu Zanga Zanga Shekara 1 da Hawa Mulki

Abuja - Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta gamu da fushin mutane musamman matasa saboda tsadar rayuwa da matsin lamba.

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Abubuwa da-dama su ka taru su ka jawo matasa su ka kudiri niyyar shiga zanga-zanga. Legit ta kawo maku wasu daga cikin dalilan.

Bola Tinubu
Abubuwa sun cabe za a yi wa Bola Tinubu zanga-zanga a Najeriya Hoto: @aonanuga1956
Asali: Twitter

Abubuwan da suka jawo zanga-zanga:

1. Farashin man fetur

Tsadar man fetur a sanadiyyar janye tallafi ya taimaka wajen tunzura matasa su shiga yajin aikin 1 zuwa 10 ga watan Agusta 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Duk da janye tallafin da aka yi, abin da yake kara fusata ‘yan Najeriya shi ne har yanzu ana fama da layi a gidajen mai a garuruwa.

Kara karanta wannan

Tinubu ya yi jawabi inda ya dawo da tallafin mai, wutar lantarki? gaskiya ta fito

2. Tsadar dala da karyewar Naira

Ana kuka da mulkin Bola Tinubu saboda yadda farashin Dala ya tashi a sakamakon karya kudin kasar da bankin CBN ya yi tun a bara.

Tsadar dalar ya jawo farashin kayan da ake saye a ketare su ka tashi. Duk da alkawuran da ake yi, har yanzu $1 ta fi karfin N1, 500.

3. Facaka da dukiyar al’umma

Ana zargin gwamnatin tarayya da facaka da dukiyar al’umma a lokacin da ake kukan talaka ya kara hakuri da halin da ya samu kan shi.

Gwamnatin APC mai-ci ta batar da biliyoyin kudi wajen sayen motoci ban da yunkurin nemawa fadar shugaban kasa sabon jirgin sama.

4. Tsare-tsaren gwamnatin Tinubu

BBC ta ce an dauki matakai domin ganin an rage radadin da ake ciki, wasu daga cikin dabarun sun hada da rabon kayan abinci a jihohi.

Sai dai mutane da yawa sun soki wannan kokari, su na ganin tallafin bai kai ga inda ake bukata kuma ba zai iya magance matsalar yunwa ba.

Kara karanta wannan

Sheikh Abdulaziz Dutsen Tanshi ya fadawa Tinubu mataki 1 da zai cire talaka daga wahala

5. Tsada da tashin farashin kaya

Ganin yadda kaya musamman abinci su ka tashi a kasuwa ya harzuka mutane. Aljazeera ta ce ana ganin akwai laifin manufofin Bola Tinubu.

Magidanta sun ce mana ba su iya yin cefane a halin da ake ciki. Ana bukatar akalla N3000 a kullum yayin da hanyoyin samu suka tsuke a yau.

6. Zargin rashin gaskiya

Akwai jami’an gwamnati da ake tuhuma da rashin gaskiya amma ba a ji irinsu hukumomin EFCC, ICPC, NFIU da sauransu sun yi nasara a kansu ba.

Legit ta lura shirin da aka ji game da wadanda ake bincike bai yi wa jama’a dadi sannan ana zargin EFCC ta buge da kama masu kananan laifi.

7. Jinkirin karin albashi

Daidai lokacin da rayuwa tayi kunci, an yi tunanin gwamnatin tarayya a karkashin jagorancin Bola Tinubu za ta kara albashin ma’aikata.

An shafe watanni ba a kai ga karin albashin ba duk da an amince da karin N70, 000 a majalisa. A baya an yi ta kokarin biyan ma’aikata N35, 000.

Kara karanta wannan

Ku kara hakuri: Ministan Tinubu ya ba 'yan Arewa shawari kan zanga-zangar da ake shirin yi

Yunkurin hana zanga-zanga

Yayin da aka hango hadarin zanga-zanga, rahoto ya zo cewa a gurguje gwamnati ta amince da kudirin mafi karancin albashi da wasu matakai.

Wasu suna alakanta daukar aikin da ake shirin yi a NNPC da ba kananun hukumomi 'yancin kai duk a yunkurin hana matasa zanga-zanga.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng