Bayan Kamfanin NNPCL ya Bayyana Shirin Daukar Aiki, Shafinsa ya Tsaya Cak

Bayan Kamfanin NNPCL ya Bayyana Shirin Daukar Aiki, Shafinsa ya Tsaya Cak

  • Kamfanin mai na kasa, NNPCL ya bayyana cewa ya bude kofar daukar ma'aikata da za su taimaka wajen cigaban ayyukan shi
  • Awanni da wallafa shafin da jama'a za su shiga domin nuna sha'awar a dauke su aiki a kamfanin ne kuma aka gano ba ya yi
  • Kamfanin ya dawo ya yi karin bayanin cewa jama'a ne su ka yiwa shafin yawa, shi ya sa aka fuskanci matsala amma za a dauki mataki

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Kamfanin mai na kasa (NNPCL) ya bayyana cewa ya yi shirin fara daukar ma'aikata a matakai daban-daban domin aiki a kamfanin.

Kara karanta wannan

"A rungumi zaman lafiya": Malam Izala da Darika sun yi magana bayan ganawa da Tinubu

Sai dai bayan wallafa wannan sanarwa a shafukan sada zumuntar NNPCL ne aka gano cewa shafin da aka bayar ba ya aiki.

Mr Mele Kolo Kyari Fans
Shafin daukar aikin kamfanin NNPCL ya tsaya da aiki Hoto: Mr Mele Kolo Kyari Fans
Asali: Facebook

Kamfanin NNPCL ya wallafa a shafinsa na X cewa zai ci gaba da karbar bukatar daukar aiki daga 'yan Najeriya har 20 Agusta, 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

NNPCL: Shafin daukar aiki ba ya yi

Bayan wallafa tallar daukar mutane aiki a kamfanin NNPCL, 'yan Najeriya da su ka shiga shafin sun gano ba ya aiki.

Wasu da su ka wallafa sakonnin su a shafin Facebook na kamfanin sun zarge su da kokarin fito da shirin da zai kawar da hankalin 'yan kasa daga zanga-zanga.

Collins A Atoberuru ya ce ;

" Mutane sun yi magana da murya daya, ban taba ganin inda NNPC ta bayyana shirin daukar aiki ga jama'a ba, amma yanzu tsoron zanga-zangar gama gari."

Kara karanta wannan

Shugaban NNPCL, Kyari ya yi zazzafan martani ga Dangote kan kalamansa

NNPCL ya fadi dalilin tsayawar shafinsa

Kamfanin NNPCL ya bayyana dalilin da ya sa aka samu matsala da shafinsa da ya wallafa na daukar jama'a aiki.

A sakon da kamfanin ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bayyana cewa cunkosun mutane ne ya tsayar da shafin, amma ta kokarin gyara.

Kamfanin NNPCL ya fadi dalilin tsadar mai

A baya kun ji cewa shugaban kamfanin man fetur na kasa ( NNPCL) ya bayyana dalilin da ya sa ake samun dogayen layin fetur a gidajen mai da ke fadin kasar nan.

Kamfanin ya dora alhakin hakan a kan mamakon ruwan sama da aka samu, inda ya kara da cewa ya kawo tsaiko wajen safarar fetur zuwa gidajen mai.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.