Gwamnan APC Ya Tsure, Ya Bayyana Fargabarsa a Kan Shirin Zanga Zangar Lumuna

Gwamnan APC Ya Tsure, Ya Bayyana Fargabarsa a Kan Shirin Zanga Zangar Lumuna

  • Bayan dagewa da masu shirin zanga-zanga su ka yi a kan lallai sai sun nuna bacin ransu ga gwamnati, gwamnatin Legas ta bayyana fargaba
  • Sakatariyar gwamnatin jihar, Barista Bimbola Salu Hundeyin ta bayyana cewa akwai fargabar za a iya jawo asarar dukiyoyi da rayukan jama'a
  • Ta ce bai kamata a gudanar da zanga-zanga a jihar Legas ba, ganin yadda gwamnatin ta yi kokari wajen inganta rayuwar mazauna cikinta

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Legas - Yayin da gwamnati ta ga yadda jama'ar kasar nan su ka dage a kan tsunduma zanga-zanga, gwamnatin jihar Legas ta fara kiraye-kiraye gudanar da ita cikin lumana.

Kara karanta wannan

Gwamnati ta bayyana jihar Arewa da ba za a yi zanga zanga ba

Gwamnatin ta gargadi wadanda ke da niyyar fitowa daga ranar 1 Agusta, 2024 domin yin zanga-zanga da su tabbata sun guji lalata kadarori ko tayar da hankula.

Bola Tinubu
Gwamnatin Legas ta nemi a yi zanga zanga cikin lumana Hoto: Babajide Sanwo-Olu
Asali: Facebook

Jaridar Vanguard ta tattaro cewa jihar Legas ta bakin sakatariyar gwamnati, Barista Bimbola Salu Hundeyin ce ta yi gargadin yayin wani taro da sakatarorin kananan hukumomi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnati ta shiga damuwa kan zanga zanga

Gwamnatin jihar Legas ta shiga damuwa a kan shirin zanga-zangar gama gari ta kwanaki 15 da wasu 'yan Najeriya ke shirin yi.

Sakatariyar gwamnatin jihar, Barista Bimbola Salu Hundeyin ce ta bayyana damuwar, inda ta ce akwai fargabar za a iya lalata dukiyoyi da jawo asarar rayuka, Daily Post ta wallafa.

Ta ce duk da cewa zanga-zanga 'yancin kowanne dan kasa ce, bai kamata a gudanar da ita a jihar Legas da ta yiwa jama'a aikin da ya kamata ba.

Kara karanta wannan

Gwamnonin jihohi 36 sun yi magana kan zanga zangar da matasa ke shirin yi

Zanga-zanga: Sanata Ndume ya shawarci Tinubu

A baya kun ji cewa Sanata mai wakiltar Kudancin Borno a majalisa, Ali Ndume ya shawarci gwamnatin Bola Ahmed Tinubu a kan yadda za ta gujewa faruwar zanga-zanga.

Sanata Ali Ndume ya nemi shugaban kasa da mukarrabansa su zauna a kan teburin sulhu da wakilan matasan kasar nan domin lalube mafita mafi sauki a maimakon zanga-zanga.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.