Shugaba Tinubu Ya Mika Kudirin Sabon Mafi Karancin Albashi ga Majalisa, Bayanai Sun Fito

Shugaba Tinubu Ya Mika Kudirin Sabon Mafi Karancin Albashi ga Majalisa, Bayanai Sun Fito

  • Bola Ahmed Tinubu ya aika kudirin sabon mafi ƙarancin albashin ma'aikata na N70,000 ga majalisar wakilai ranar Talata, 23 ga watan Yuli
  • Shugaban ƙasar ya buƙaci ƴan majalisar su gaggauta amincewa da kudirin sabon albashin domin aiwatar da shi a kan lokaci
  • Haka nan Tinubu ya bukaci majalisar ta yi wa kundin dokokin rundunar ƴan sandan Najeriya garambawul kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da kudirin sabon mafi karancin albashi ga majalisar wakilai domin tantancewa tare da amincewa da shi.

Ana sa ran kudirin dokar zai zaratar da mafi karancin albashi na N70,000 wanda aka amince da shi kwanan nan ya zama doka a Najeriya.

Kara karanta wannan

N70,000: Ƴan aikin gida za su sha romo, majalisa da ƙungiyar NCWS sun miƙa bukata

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.
Shugaba Tinubu ya Gabatar da kudirin mafi ƙarancin albashi a Majalisa Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Twitter

Shugaba Bola Tinubu ya kai kudirin albashi

The Nation ta ce Idan baku manta ba gwamnatin tarayya, kamfanoni masu zaman kansu da kungiyoyin kwadago sun cimma matsaya kan N70,000 ranar Alhamis da ta wuce.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wasikar shugaban wadda aka karanta a zauren majalisar yau Talata, ta ƙunshi sabon albashi mafi karanci na N70,000 da kuma tsarin aiwatar da shi, Channels tv ta rahoto.

Bola Tinubu ya roƙi ‘yan majalisar su gaggauta amincewa da kudurin dokar domin fara aiwatar da shi a kan lokaci kuma ma'aikatan gwamnati su fara cin gajiya.

Tinubu ya nemi gyara dokar ƴan sanda

Bayan haka Shugaban ya miƙa bukatar yiwa dokar rundunar ƴan sanda garambawul ga majalisar wakilai ta ƙasa.

Ya roƙi ‘yan majalisar su yi wa dokar ƴan sanda garambawul kamar yadda sashe na 58 na kundin tsarin mulkin kasa na 1999 ya tanada.

Kara karanta wannan

Sanata Ndume ya yi magana kan batun zanga zangar matasa, ya kawo mafita 1

Abin da shugaban kasar ya buƙaci gyara shi ne dokokin rundunar ‘yan sanda dangane da nadi da kuma wa’adin ofishin Sufeto Janar na ‘yan sanda.

Ƴan aiki za su sha romon karin albashi

A wani labarin kuma Majalisar dattawa tare da kungiyar NCWS sun bukaci a sanya ƴan aikin gida a tsarin sabon mafi ƙarancin albashi na N70,000.

Kwamitin kwadago da samar da ayyukan yi na majalisar dattawa ya ce ya kamata ƴan aiki su amfana da sabon albashi mafi karanci na ƙasa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262