N70,000: Ƴan Aikin Gida Za Su Sha Romo, Majalisa da Ƙungiyar NCWS Sun Miƙa Bukata
- Majalisar dattawa tare da kungiyar NCWS sun bukaci a sanya ƴan aikin gida a tsarin sabon mafi ƙarancin albashi na N70,000
- Kwamitin kwadago da samar da ayyukan yi na majalisar dattawa ya ce ya kamata ƴan aiki su amfana da sabon albashi mafi karanci na ƙasa
- Shugaban kwamitin, Sanata Diket Plang ya ce za a kafa hukumar da za tabbatar da an aiwatar da wannan doka
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja - Majalisar Dattawa da Ƙungiyar Mata ta Kasa (NCWS) sun nemi a saka masu aikin gida a cikin tsarin sabon mafi karancin albashi na N70,000.
Hakan na ɗaya daga cikin abubuwan da aka ambata a taron jin ra'ayoyin jama'a wanda kwamitin kwadago da samar da ayyukan yi ya shirya a Abuja.

Kara karanta wannan
Shugaba Tinubu ya miƙa kudirin sabon mafi ƙarancin albashi ga majalisa, bayanai sun fito

Asali: Facebook
Yan aiki za su samu karin albashi?
Kamar yadda Channels tv ta ruwaito, an yi taron jin ra'ayoyin jama'a ne kan kudirin inganta ayyukan ƴan aiki da yi masu rijista a Najeriya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sanata mai wakiltar Imo ta Yamma, Osita Izunaso da shugabar NCWS, Geraldeen Etuk ne suka nemi sanya ma'aikatan cikin gida a dokar mafi karancin albashi na kasa.
Ma'aikatan cikin gida sun haɗa da ƴar aiki, direba da sauran masu yiwa mutane hidimi a cikin gida.
Majalisa za ta kawo batun karin albashi
Da yake jawabi, Sanata Izunaso ya ce:
"A matsayin 'dan wannan kwamiti, ina jin cewa wani bangaren da za a sanya a cikin wannan kudiri shi ne sanya ma’aikatan gida walau ‘yar aiki ko kuma masu hidima a dokar mafi karancin albashi na N70,000.”
"Tun da an amince N70,000 ya zama albashin ƙananan ma'aikata mafi ƙaranci, ya kamata ma'aikatan gida su shiga ciki, zamu sa batun a kudirin domin aiwatarwa."
Shugaban kwamitin Sanata Diket Plang ya kuma bayyana cewa za a kafa wata hukuma ta musamman da za ta sa ido da tabbatar da aiwatar da dokar, Arise tv ta tattaro.
Sanata Kalu ya koka kan albashinsu
A wani rahoton kuma Sanata wai wakiltar jihar Anambara, Orji Uzo Kalu ya koka kan yadda ake biyan Sanatoci kudi kadan a matsayin albashi
Bayan haka, Sanata Orji ya bukaci a canza tsarin zaman majalisa yadda zai dace da kudin da ake biyansu a matsayin albashi a kowane wata.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng