"Ku Shirya," Kungiyar Amnesty Int'l ta Tura Sako ga Gwamnati kan Zanga Zanga

"Ku Shirya," Kungiyar Amnesty Int'l ta Tura Sako ga Gwamnati kan Zanga Zanga

  • Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta shawarci gwamnatin Najeriya kan yadda za ta bullo wa batun zanga-zanga
  • Shugaban kungiyar na Najeriya, Mista Isa Sanusi ya shaida wa Legit cewa ba a hana zanga-zanga idan jama'a sun ce za su yi ba
  • Amma ya bayyana cewa akwai matakai da gwamnatin tarayya ya kamata ta dauka domin dakile rikidersa wa zuwa tashin hankali

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano - Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International (AI) ta shawarci gwamnatin tarayya kan yadda za ta bullowa lamarin zanga-zanga da wasu ke shirin yi a kasar nan.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Kungiyar Amnesty Intl ta caccaki gwamnati kan kama 'dan gwagwarmyan Tiktok

A tattaunawar shugaban kungiyar na Najeriya, Isa Sanusi da Legit, ya ce gudanar da zanga-zanga ba haramun ba ce, kuma akwai nauyi da ya rataya a wuyan gwamnati a irin lokutan.

Zanga zanga
AI ta shawarci gwamnatin Najeriya kan ba wa masu niyyar zanga-zanga tsaro Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu/Isa Sanusi
Asali: Facebook

Shugaban Amnesty Int'l ya ce dole ne gwamnatin tarayya da jami'an tsaro su tabbatar an kare rayuka da duniyoyin masu gudanar da zanga-zanga, idan har hakan ta kasance.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Zanga zanga ba haramun ba ce," Amnesty Int'l

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta ce ba ta dauki zanga-zanga a matsayin abu mai illa ba.

Shugaban kungiyar na kasar nan, Isa Sanusi ya ce tsarin mulkin Najeriya bai haramta a gudanar da zanga-zanga ba, amma dai akwai sharuda.

Ya ce sharadin shi ne ya zama zama zanga-zanga ce ta lumana wacce ba sace-sace, babu kona dukiya, babu zage-zage, babu hauragiya.

Kara karanta wannan

Matasan Arewa sun soki Ministan Buhari kan goyon bayan zanga zanga

"Sannan ita ma gwamnati ta na da hakki. Domin idan mutum ya ce zai yi zanga-zanga, hakkin gwamnati ne ta ba shi kariya, sannan ta tabbatar da cewar ya yi ta a cikin lumana ba tare da wani ya zo ya shiga ciki ya bata masa zanga-zangar ba kuma ta zo ta rikide ta zama tashin hankali."

-Isa Sanusi, Shugaban AI na Najeriya.

"Ba a hana zanga-zanga," Amnesty Int'l

Kungiyar AI ta shawarci gwamnatin Najeriya kan cewa ba hana zanga-zanga ake yi ba idan jama'a sun kuduri aniyar gudanar da ita.

Shugaban kungiyar na kasa ya ce kokari ake yi a nusar da jama'a yadda za su gudanar da ita cikin lumana da kwanciyar hankali tare da kare lafiyarsu.

Katsina: An yi zanga-zanga kan rashin tsaro

A wani rahoton kun ji cewa wasu mazauna karamar hukumar Kankara a jihar Katsina sun gudanar da zanga-zanga kan rashin tsaro da ya hana su sakat.

Kara karanta wannan

Shiga jami'a: Duk da dage kayyade shekarun dalibai, tsohon Sanata ya taso gwamnati a gaba

Mazauna yankin sun rufe manyan hanyoyin da ake bi a bangarensu ciki har da mararrabar Katsina zuwa Kano, tare da bukatar mahukunta su gaggauta kawo masu agaji kan yan ta'adda.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.