"Ku Shirya," Kungiyar Amnesty Int'l ta Tura Sako ga Gwamnati kan Zanga Zanga

"Ku Shirya," Kungiyar Amnesty Int'l ta Tura Sako ga Gwamnati kan Zanga Zanga

  • Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta shawarci gwamnatin Najeriya kan yadda za ta bullo wa batun zanga-zanga
  • Shugaban kungiyar na Najeriya, Mista Isa Sanusi ya shaida wa Legit cewa ba a hana zanga-zanga idan jama'a sun ce za su yi ba
  • Amma ya bayyana cewa akwai matakai da gwamnatin tarayya ya kamata ta dauka domin dakile rikidersa wa zuwa tashin hankali

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano - Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International (AI) ta shawarci gwamnatin tarayya kan yadda za ta bullowa lamarin zanga-zanga da wasu ke shirin yi a kasar nan.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Kungiyar Amnesty Intl ta caccaki gwamnati kan kama 'dan gwagwarmyan Tiktok

A tattaunawar shugaban kungiyar na Najeriya, Isa Sanusi da Legit, ya ce gudanar da zanga-zanga ba haramun ba ce, kuma akwai nauyi da ya rataya a wuyan gwamnati a irin lokutan.

Zanga zanga
AI ta shawarci gwamnatin Najeriya kan ba wa masu niyyar zanga-zanga tsaro Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu/Isa Sanusi
Source: Facebook

Shugaban Amnesty Int'l ya ce dole ne gwamnatin tarayya da jami'an tsaro su tabbatar an kare rayuka da duniyoyin masu gudanar da zanga-zanga, idan har hakan ta kasance.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Zanga zanga ba haramun ba ce," Amnesty Int'l

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta ce ba ta dauki zanga-zanga a matsayin abu mai illa ba.

Shugaban kungiyar na kasar nan, Isa Sanusi ya ce tsarin mulkin Najeriya bai haramta a gudanar da zanga-zanga ba, amma dai akwai sharuda.

Ya ce sharadin shi ne ya zama zama zanga-zanga ce ta lumana wacce ba sace-sace, babu kona dukiya, babu zage-zage, babu hauragiya.

"Sannan ita ma gwamnati ta na da hakki. Domin idan mutum ya ce zai yi zanga-zanga, hakkin gwamnati ne ta ba shi kariya, sannan ta tabbatar da cewar ya yi ta a cikin lumana ba tare da wani ya zo ya shiga ciki ya bata masa zanga-zangar ba kuma ta zo ta rikide ta zama tashin hankali."

Kara karanta wannan

Matasan Arewa sun soki Ministan Buhari kan goyon bayan zanga zanga

-Isa Sanusi, Shugaban AI na Najeriya.

"Ba a hana zanga-zanga," Amnesty Int'l

Kungiyar AI ta shawarci gwamnatin Najeriya kan cewa ba hana zanga-zanga ake yi ba idan jama'a sun kuduri aniyar gudanar da ita.

Shugaban kungiyar na kasa ya ce kokari ake yi a nusar da jama'a yadda za su gudanar da ita cikin lumana da kwanciyar hankali tare da kare lafiyarsu.

Katsina: An yi zanga-zanga kan rashin tsaro

A wani rahoton kun ji cewa wasu mazauna karamar hukumar Kankara a jihar Katsina sun gudanar da zanga-zanga kan rashin tsaro da ya hana su sakat.

Mazauna yankin sun rufe manyan hanyoyin da ake bi a bangarensu ciki har da mararrabar Katsina zuwa Kano, tare da bukatar mahukunta su gaggauta kawo masu agaji kan yan ta'adda.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng