Ndume: Daurawa Ya Nuna Fargaba Kan Gwamnatin Tinubu, Ya Fadi Illar Haka Gare Su

Ndume: Daurawa Ya Nuna Fargaba Kan Gwamnatin Tinubu, Ya Fadi Illar Haka Gare Su

  • Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya nuna damuwa kan yadda ake gudanar da mulki a wannan gwamnatin ta Bola Tinubu
  • Daurawa ya nuna fargaba kan yadda ake dakatarwa ko korar wadanda suke kokarin fadar gaskiya game da halin da ake ciki
  • Malamin ya ce abin tsoro ne matuka wadanda suke zaton za su jagorance su wurin Tinubu ana daukar irin wannan mataki kansu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya nuna fargaba kan gwamnatin Bola Tinubu.

Malamin ya ce abin ya fara ba shi tsoro ganin yadda ake gudanar da gwamnatin a yanzu duk da halin da ake ciki.

Kara karanta wannan

Shugaban APC Abdullahi Ganduje ya fadi dalilin karuwar cin hanci da rashawa

Daurawa ya sha jinin jikinsa da gwamnatin Bola Tinubu
Sheikh Aminu Daurawa ya koka yadda ake gudanar da mulki. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa.
Asali: Facebook

Daurawa ya fara firgita da mulkin Tinubu

Shehin malamin ya bayyana haka da safiyar yau Alhamis 18 ga watan Yulin 2024 a shafinsa na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Daurawa ya ce lamarin kasar ya fara ba shi tsoro musamman yadda ake kora ko dakatar da wadanda suke sa ran yi musu jagoranci zuwa fadar shugaban kasa.

Ya ce abin da ya faru ya firgita shi inda ya ce anya kuwa akwai adalci ko tausayin talakawa a zukatan shugabanni.

"Abin da ya faru ya ba ni tsoro."
"Irin mutanen da muke fata za su yi mana jagotanci zuwa wurin shugaban kasa domin isar da sakon al'umma an fara korasu da dakatar da su daga mukamansu."
"An yi haka ne saboda sun koka kan halin da ake ciki, anya kuwa akwai tausayi da adalci a cikin zukatansu kan talakawa?"

Kara karanta wannan

Hana zanga zanga: Malamai sun gana da Tinubu, an gano duka abubuwa 3 da aka tattauna

- Aminu Ibrahim Daurawa

An dakatar da Sanata Ndume daga mukaminsa

Wannan martani na Daurawa bai rasa nasaba da dakatar da Sanata Ali Ndume a matsayin shugaban masu tsawatarwa a Majalisar.

Majalisar ta dakatar da Ndume bayan ya caccaki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ganin yadda ake cikin halin kunci.

'Yan Majalisa sun ki hukunta Ndume

Kun ji cewa mambobin Majalisar Dattawa da dama sun ki amincewa da bukatar hukunta Sanata Ali Ndume daga jihar Borno.

Sanatocin Majalisar sun yi tawaye kan bukatar hukunta Ali Ndume bayan ya fadi munanan kalamai gare su bayan an dakatar da shi.

Sanata Fasuyi Cyril da ke wakiltar Ekiti ta Arewa shi ya bukaci hukunta Ndume inda sanatoci suka hada baki da kin amincewa da haka.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.