'Yan Bindiga Sun Sako Mahaifiyar Mawaki Dauda Kahutu Rarara, Bayanai Sun Fito

'Yan Bindiga Sun Sako Mahaifiyar Mawaki Dauda Kahutu Rarara, Bayanai Sun Fito

  • Bayan shafe akalla kwanaki 20 a hannun 'yan bindiga, mahaifiyar fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara ta samu 'yanci
  • Mawaki Rarara ne da kansa ya fitar da sanarwar kubutar mahaifiyarsa daga hannun 'yan bindigar a safiyar ranar Laraba
  • Sai dai Rarara bai yi wani ƙarin bayani game da yadda aka sako mahaifiyarsa ba, bayan rahoto ya nuna 'yan bindigar sun nemi kudin fansa

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Rahotannin da muke samu yanzu na nuni da cewa 'yan bindiga sun sako mahaifiyar fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara bayan shafe akalla mako 2 a tsare.

A ranar Juma'a, 28 ga watan Yunin 2024 muka ruwaito cewa 'yan bindiga sun kutsa sabon gidan Rarara da ke gabashin Kahutu a ƙaramar hukumar Ɗanja inda suka sace mahaifiyarsa.

Kara karanta wannan

Zamfara: Mata 5 sun tsere daga hannun 'yan bindiga, an yi jana'izar wasu mutum 5

Dauda Kahutu Rarara ya yi magana kan dawowar mahaifiyarsa
'Yan bindiga sun sako mahaifiyar mawaki Dauda Kahutu Rarara. Hoto: Dauda Kahutu Rarara
Asali: Instagram

'Yan bindiga sun sako mahaifiyar Rarara

Fitaccen mawakin, Rarara ne ya sanar da kubutar mahaifiyarsa a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Instagram a safiyar ranar Laraba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rarara ya ce:

"Cikin yarda da amincin Ubangiji mun samu dawowar mama cikin aminci."

Mawakin ya kuma mika godiya ta musamman ga abokan sana'arsa da ma masoyansa baki daya bisa irin kulawar da suka nuna masa da taya shi alhinin sace mahaifiyarsa da aka yi.

Sai dai Dauda Kahutu Rarara bai yi wani ƙarin bayani ba game da yadda aka sako mahaifiyarsa, da kuma bayyana ko sai da aka biya kuɗin fansa kafin sakinta.

Mai magana da yawun Rarara a kafofin watsa labarai, Rabi'u Garba Gaya, ya wallafa bidiyon Rarara tare da mahafiyarsa bayan kubutarta.

Kalli bidiyon a nan kasa:

An nemi kudin fansar mahaifiyar Rarara

Kara karanta wannan

Gwamna ya aike da saƙo bayan ɗan majalisar tarayya daga Kaduna ya rasu

A wani labarin, mun ruwaito cewa 'yan bindigan da suka sace mahaifiyar Dauda Adamu Kahutu wanda aka fi sani da Rarara sun faɗi kuɗin fansan da za a ba su.

An ce 'yan bindigan sun buƙaci da a biya su Naira miliyan 900 a matsayin kuɗin fansa kafin su sako Hajiya Halima Adamu wacce suka sace a Kahutu.

Bayan sun bayyana kudin da suke so, sun kuma ba iyalan Hajiya Halima tabbacin cewa tana cikin ƙoshin lafiya sannan za a sake ta da zarar an biya kuɗaɗen.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.