Kakar Zabe: INEC Ta Sanar da Daukar Sababbin Ma’aikata, Ta Fadi Matakan Neman Aikin

Kakar Zabe: INEC Ta Sanar da Daukar Sababbin Ma’aikata, Ta Fadi Matakan Neman Aikin

  • Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta sanar da bude guraben ma’aikatan wucin gadi a zaben gwamna da ke tafe a jihohin Ondo da Edo
  • A cewar INEC, guraben da aka bude na daukar ma’aikatan wucin gadi sun hada da mukamin SPOs, POs, APOS, RATECHs da kuma RACs
  • Hukumar zaben ta sanya takunkumi kan masu neman aikin da suke cikin harkar siyasa dumu-dumu da kuma bayyana ka'idojin neman aikin

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta sanar da bude guraben daukar ayyukan wucin gadi domin shiryawa zaben gwamna da ke tafe a jihohin Edo da Ondo.

Kara karanta wannan

Wahalar fetur za ta tsananta, dillallan mai sun shiga yajin aiki a wasu jihohin Najeriya

A cewar INEC, guraben da aka bude na daukar ma’aikatan wucin gadi sun hada da mukamin SPOs, POs, APOS, RATECHs da kuma RACs.

INEC ta sanar da bude guraben ma'aikatan wucin gadi na zaben gwamnoni jihohin Edo da Ondo.
INEC ta bayyana sababbin guraben aikin wucin gadi a zaben gwamnan Edo da Ondo. Hoto: @inecnigeria
Asali: Twitter

INEC: Yadda za ka nemi aikin wucin gadi

A cewar sanarwar da hukumar zaben ta wallafa a shafinta na X, ta ce masu sha'awar yin aikin za su iya yin rijistar neman aikin ta shafinta na INECPRES.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce za a bude shafin INECPRES daga ranar Litinin 15 ga watan Yuli zuwa Litinin 19 ga watan Agusta, 2024, da misalin karfe 12:00 na dare.

INEC ta ce masu amfani da kwamfuta za su iya yin rajista ta shafin http://pres.inecnigeria.org, yayin da masu son yin rajista ta wayar Android za su ziyarci https://inecpres-app.com.

INEC ta kawo ka'idojin neman aiki

Domin samun cancantar yin aiki a matsayin ma'aikacin wucin gadi na INEC a zaɓen gwamnonin Edo da Ondo, dole ne masu neman aikinsu cika wadannan ka'idodin na kasa:

Kara karanta wannan

Ana dab da zabe: An harbi tsohon shugaban kasar Amurka Donald Trump a wani taro a Pennsylvania

  • Ka da su kasance mambobin jam'iyyar siyasa.
  • Ka da su nuna goyon bayansu ga kowane dan takara ko jam'iyya.
  • Dole ne su kasance mazauna jihohin da za ayi zaben (ban da masu neman mukamin RATECHs).

Duba sanarwar INEC a kasa:

APC ta fidda dan takarar gwamnan Ondo

A wani labarin, mun ruwaito cewa Gwamna Lucky Aiyedatiwa na jihar Ondo ya lashe zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC da aka gudanar a jihar.

Aiyedatiwa, wanda ya gaji marigayi Rotimi Akeredolu a watan Disamba, ya yi nasara kan ƴan takara 15 a zaɓen fidda gwanin da aka gudanar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.