Tinubu Ya Rikita Najeriya da Mukamai, Ya Sake Nada Dan Tsohon Gwamna a Arewa Mukami

Tinubu Ya Rikita Najeriya da Mukamai, Ya Sake Nada Dan Tsohon Gwamna a Arewa Mukami

  • Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi ruwan mukamai a jiya Asabar 13 ga watan Yulin 2024 a hukumomi daban-daban
  • Shugaban ya nada dan tsohon gwamnan jihar Kwara, Cornelius Oluwasegun Adebayo a matsayin shugaban NALDA
  • Hadimin shugaban a bangaren yada labarai, Ajuri Ngelale shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Asabar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin dan tsohon gwamnan jihar Kwara, Cornelius Oluwasegun Adebayo mukami.

Tinubu ya nada Adebayo ne a matsayin shugaban hukumar ci gaban harkokin noma da aka fi sani da NALDA.

Tinubu ya nada dan tsohon gwamnan Kwara shugaban hukumar NALDA
Bola Tinubu ya nada Cornelius Oluwasegun Adebayo shugaban hukumar NALDA. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

TinUbu ya nada sabon shugaban hukumar NALDA

Kara karanta wannan

Kano: Bayan nadin Dan Agundi, Tinubu ya nada surukin Ganduje babban muƙami

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hadimin shugaban, Ajuri Ngelale ya fitar a shafinsa na Facebook a jiya Asabar 13 ga watan Yulin 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Adebayo 'da ne ga tsohon gwamnan Kwara, Cif Cornelius Adebayo wanda ya mulki jihar a shekarar 1983.

Shugaban ya bukaci Adebayo da ya yi amfani da kwarewarsa wurin tabbatar kawo ci gaba a hukumar da kuma bangaren noma baki daya.

"Shugaba Tinubu ya bukaci shugaban hukumar NALDA da ya yi mafani da kwarewarsa da hikima wurin kawo ci gaba a harkokin noma."

- Ajuri Ngelale

Tinubu ya nada surukin Ganduje mukami

Wannan na zuwa ne bayan nadin surukin tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje a matsayin hadimi na musamman ga shugaban.

Tinubu ya amince da nadin Idris Ajimobi a matsayin hadiminsa na musamman a bangaren kula da kiwon dabbobi.

Kara karanta wannan

Batun gyara ake: Tinubu ya sake kora a hukumomi, ya nada sabbin shugabanni a PenCom, NSITF

Nadin na zuwa ne bayan kirkirar sabuwar ma'aikata a Abuja da za ta kula da ci gaban noma da kuma kiwon dabbobi.

Tinubu ya nada Dan Agundi mukami

A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya nada Baffa Dan Agundi a matsayin shugaban hukumar kula da nagartar ayyuka.

Tinubu ya amince da nadin ne ta bakin hadiminsa a bangaren yada labarai, Ajuri Nglale a jiya Asabar 13 ga watan Yulin 2024.

Shugaban ya kuma amince da nadin tsohon sanatan Kano ta Tsakiya, Bashir Lado a matsayin hadiminsa a Majalisar Dattawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.