Gwamnatin Tinubu Ta Dauki Matakin Magance Yunwar da Ake Yi a Kasa

Gwamnatin Tinubu Ta Dauki Matakin Magance Yunwar da Ake Yi a Kasa

  • Gwamnatin tarayyar Najeriya na ci gaba da ƙoƙari domin magance matsalar ƙarancin abincin da ake fama da ita a ƙasar nan
  • Gwamnatin za ta aika da tireloli 60 na takin zamani ga kowace jiha domin rabawa ga manoma su yi amfani da shi a gonakinsu
  • Majalisar dattawa ce ta bayyana hakan a yayin zaman da ta yi a ranar Talata, 9 ga watan Yulin 2024 a birnin tarayya Abuja

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - A ci gaba da ƙoƙarin shawo kan matsalar ƙarancin abinci da ake fama da ita a ƙasar nan, gwamnatin tarayya ta aika da tireloli 60 na takin zamani ga kowace jiha a tarayyar ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Majalisa ta jawo hankalin Tinubu kan yunwa a kasa, ta ba shi mafita

Haka kuma kowanne Sanata daga cikin sanatoci 109 za su samu tireloli biyu na taki domin rabawa manoman mazabarsu, yayin da ƴan majalisar wakilai 360 za su samu tirela ɗaya domin rabawa a mazaɓunsu.

Gwamnatin tarayya za ta raba takin zamani
Gwamnatin tarayya za ta raba taki ga jihohi Hoto: @DOlusegun
Asali: Twitter

Majalisa ta koka kan ƙarancin abinci

Majalisar dattawa ta bayyana shirin a ranar Talata yayin da take muhawara kan matsalar ƙarancin abinci a zauren majalisar, cewar rahoton jaridar The Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majalisr ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta ɗaukar mataki kan rabon takin.

Kiran ya biyo bayan ƙudirin da Sanata Sunday Karimi, mai wakiltar Kogi ta Yamma, da Sanata Ali Ndume na Borno ta Kudu suka gabatar a zauren majalisar ranar Talata, rahoton jaridar Premium Times ya tabbatar.

A nasa tsokacin, tsohon shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya bayyana cewa ƴan Najeriya sun yi haƙuri amma ba zai iya ba da tabbacin za su iya ci gaba da jurewa ba.

Kara karanta wannan

ASUU ta bayyana abin da zai hana ta shiga yajin aiki a fadin Najeriya

Gwamnati ta ba jihohi taki

Da yake na shi tsokacin, shugaban kwamitin noma da abinci na majalisar dattawa, Sanata Saliu Mustapha (APC Kwara ta Tsakiya), ya shaida wa majalisar cewa gwamnatin tarayya ta tura takin zuwa jihoji.

"Tuni Gwamnatin Tarayya ta tura tireloli 60 na takin zamani zuwa kowace jiha ta tarayya, tireloli biyu ga kowacce mazaɓar Sanata 109 da tirela ɗaya ga kowace mazaɓar tarayya 360."

- Sanata Saliu Mustapha

Jigon APC ya ba Tinubu shawara

A wani labarin kuma, kun ji cewa jigo a jam'iyyar APC, Olatunbosun Oyintoloye ya shawarci shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gaggauta shawo kan matsalar yunwa a ƙasar nan

Ya bayyana cewa ƴan Najeriya na cikin matsi, yunwa da rashin samun kudin gudanar da harkokin rayuwarsu na yau da kullum a ƙasar nan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng