Kotu Ta Sanya Ranar Hukunci Kan Bukatar Emefiele Na Fita Waje Domin Duba Lafiyarsa

Kotu Ta Sanya Ranar Hukunci Kan Bukatar Emefiele Na Fita Waje Domin Duba Lafiyarsa

  • Hukumar hana yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati (EFCC) ta soki bukatar da tsohon gwamnan babban bankin kasa (CBN) ya shigar gaban kotu
  • Mista Emefiele na neman kotu ta bayar da izinin maido masa da fasfonsa domin ba shi damar fita kasar waje a duba lafiyarsa
  • Amma lauyan EFCC, Muhammad Abbas Omeiza ya bayyana wa kotu cewa babu shaidar da ke nuna Emefiele ba shi da lafiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa. Abuja- Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta sanya ranar 17 Yuli, 2024 domin yanke hukunci kan bukatar tsohon gwamnan babban bankin kasa, Godwin Emefiele. Mista Emefiele na neman kotu ta amince a bashi fasfo dinsa domin ya samu damar fita a duba lafiyarsa a kasar waje.

Kara karanta wannan

Zambar N80bn: Kotu ta yi watsi da bukatar Yahaya Bello na canja wurin shari'arsa da EFCC

Emefiele
Kotu za ta yanke hukunci kan rokon tsohon gwamnan CBN kan fita kasar waje duba lafiyarsa Hoto: Kola Sulaimon
Asali: Getty Images

Premium Times ta wallafa cewa tuni hukumar hana yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati (EFCC) da ke karar Emefiele ta soki bukatar.

EFCC ta soki bukatar mayarwa Emefiele fasfo

Hukumar EFCC ta ce babu wata takarda a gabanta da ke nuna cewa tsohon gwamnan babban bankin kasa (CBN) ba shi da lafiya. A sanarwar da shugaban sashen yada labarai na hukumar EFCC, Dele Oyewale ya fitar, ya ce lauyansu Muhammad Abbas Omeiza ya soki bukatar Emefiele a kotu. Muhammad Abbas Omeiza ya shaidawa kotu cewa babu wata shaida da ke nuna rashin lafiyar wanda ake kara, Channels Television ta wallafa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kara da cewa ko da ta tabbata Mista Emefiele na fama da rashin lafiya, babu wata hujja da ta nuna ba zai samu kulawa a cikin Najeriya ba.

Bayan sauraron bangarorin biyu, Mai Shari'a Hamza Mu’azu ya sanya ranar 17 Yuli, 2024 domin yanke hukunci kan bukatar.

Kara karanta wannan

Auren jinsi: Yadda kururuwar mutanen Kano ya dakile yunkurin kungiyar LGBTQ

Emefiele ya ki amincewa da tuhumar EFCC

A wani labarin kun ji cewa tsohon shugaban babban bankin kasa (CBN), Godwin Emefiele ya musanta zarge-zargen da hukumar EFCC ke yi masa.

EFCC na zargin Mista Emefiele da laifin amfani da N18.96b wajen buga kudade N684.5m, amma ya musanta zargin, lamarin da ya sa kotu ta bayar da bakinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.