An Bankado Yadda Sambo Dasuki Ya Ba Tsohon Gwamna N1.2bn Daga Kudin Makamai

An Bankado Yadda Sambo Dasuki Ya Ba Tsohon Gwamna N1.2bn Daga Kudin Makamai

  • Mai ba da shaida kuma mai bincike a hukumar EFCC ya ba da shaidar yadda Sambo Dasuki ya tura makudan kudi ga tsohon gwamna
  • Abubakar Madaki ya ce Dasuki ya tura kudi har N1.2bn ga Ayo Fayose domin batar da inda asali kudin suka fito da ake zargi na makamai ne
  • Hakan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da binciken tsohon gwamnan na jihar Ekiti, Fayose kan badakalar N6.9bn lokacin mulkinsa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Yayin da ake ci gaba da shari'ar tsohon gwamnan Ekiti, Ayodele Fayose, an bankado wata badaƙala.

Wani mai ba da shaida a kotu ya bayyana yadda tsohon mai ba da shawara a harkokin tsaro, Sambo Dasuka ya ba Fayose N1.2bn.

Kara karanta wannan

"Muna tsoron faruwar irin zanga-zangar Kenya": Jigon APC ya gargadi Tinubu

An bankado wata bada tsakanin Dasuki da Fayose
An zargi Sambo Dasuki da turawa Ayodele Fayose N1.2bn na kuɗin makamai. Hoto: Economic and Financial Crimes Commission.
Asali: Facebook

EFCC: An gano badakalar Dasuki da Fayose

Abubakar Madaki, mai bincike a EFCC ya fadawa alkalin kotun, Chukwujekwu Aneke cewa Dasuki ya ba Fayose kudin domin batar da ainihin tushensu, cewar hukumar EFCC.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tuhumar tsohon gwamna Fayose kan badakalar N6.9bn.

Tun farko, hukumar EFCC ta gurfanar da Fayose a gaban kotu a watan Yulin 2019 kan tuhume-tuhume har guda 11.

Yadda EFCC ta gano badakalar Sambo Dasuki

Har ila yau, tun farkon shari'ar, tsohon Ministan tsaro, Musiliu Obanikoro ya fadawa kotun cewa Dasuki ya umarce shi da ya tura kudin har N1.2bn.

Obanikoro ya ce an umarce shi ya tura kudin ne daga asusun tallafi na musamman na Boko Haram.

Madaki ya ce ba kamar yadda Fayose ya yi ikirari ba cewa kudin kamfen PDP ne, an gano daga cikin kudin makamai suke a mulkin Goodluck Jonathan.

Kara karanta wannan

Kano: Dalilai 3 da za su hana Aminu Ado Bayero ƙwace sarauta daga hannun Sanusi II

Fayose ya tona asirin basukan Buhari

A wani labarin, kun ji cewa tsohon gwamnan Ekiti, Ayodele Fayose ya soki yadda tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya yi mulkin kasar.

Fayose ya bayyana haka a wata hira da aka yi da shi inda ya zargi gwamnatin Muhammadu Buhari da lalata tattalin arzikin kasar.

Tsohon gwamnan na jihar Ekiti yana ganin tsohon shugaban Najeriyan ya jawowa Najeriya ci-bayan tsawon shekaru 50 a mulkinsa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel