Kishin Ƙishin Din Kara Kudin Fetur Ya Jawo Kulle Gidajen Mai, Jama’a Sun Shiga Tasko

Kishin Ƙishin Din Kara Kudin Fetur Ya Jawo Kulle Gidajen Mai, Jama’a Sun Shiga Tasko

  • Al'ummar birnin Ibadan na jihar Oyo sun shiga babbar damuwa bayan kulle gidajen mai da yan kasuwa suka yi a jihar a safiyar yau Litinin
  • Yanayin ya jefa masu motoci, babura da Keke NAPEP rashin samun wadataccen mai wanda hakan ya kawo karancin abubuwan hawa a birnin
  • Al'ummar birnin sun bayyanawa manema labarai mummunan halin da suka shiga saboda rashin isassun abubuwan hawa bayan sun wayi gari

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Oyo - Rahotanni da ke fitowa daga birnin Ibadan sun nuna cewa an samu karancin abubuwan hawa a safiyar yau.

Bincike ya tabbatar da cewa hakan ya faru ne sakamakon kulle gidajen mai da yan kasuwa suka yi a birnin Ibadan.

Kara karanta wannan

An samu karin mutanen da suka mutu a harin bam da aka kai jihar Borno

Jihar Oyo
Kulle gidajen mai ya jefa al'umma cikin matsala a Oyo.
Asali: Original

Jaridar Tribune ta ruwaito cewa kungiyar IPMAN ta yi taro a makon da ya wuce domin duba karin kudin mai a jihohin Oyo da Osun.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rashin abubuwan hawa a Oyo

Wuraren da ake hawa mota a birnin Ibadan sun zamo kufai a safiyar yau inda aka hango al'umma sun yi carko-carko suna jiran motoci.

Haka zalika wuraren da ake samun babur da Keke NAPEP duk sun kasance da tarin jama'a amma babu abin hawa.

Ma'aikaciya ta rasa abin hawa

Wata ma'aikaciya mai suna Adenike Jayeola ta dade tana jiran abin hawa a bakin hanya amma abu ya gagara.

Adenike Jayeola ta ce babu alamar motar bas ko keke NAPEP da za ta hawu domin zuwa aiki a safiyar Litinin.

Ma'aikaci ya makara wajen zuwa aiki

Wani ma'aikaci mai suna Sanjo ya bayyana cewa ya shafe lokaci mai tsawo yana jiran abin hawa amma ya rasa, rahoton Leadership.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun buɗe wa matafiya wuta, sun yi awon gaba da mutane 20 a kan titi

Mista Sanjo ya tabbatar da cewa rashin samun abin hawa a kan lokaci ya jawo masa yin lattin zuwa wajen aiki.

Garuruwan da ake tsadar mai a Najeriya

A wani rahoton, kun ji cewa Jigar Jigawa ce ta fi ko ina tsadar man fetur a Najeriya inda ake sayar da lita daya a kan N937.50 kamar yadda rahoto ya nuna.

Hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ta ce mafi saukin farashin da 'yan Najeriya ke sayen litar man fetur ya karu zuwa N769.62.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Online view pixel