Shehu Sani Ya Fadi Matakin da Zai Dauka Kan Wike Bayan Idan Suka Hadu Nan Gaba

Shehu Sani Ya Fadi Matakin da Zai Dauka Kan Wike Bayan Idan Suka Hadu Nan Gaba

  • Tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani ya yi martani kan wasu kalamai da ministan Abuja, Nyesom Ezonwo Wike ya yi masa
  • Sanata Shehu Sani ya bayyana damar da yake jira domin ya rama abin da ya kira cin fuskar da ministan Abuja ya masa a yayin wani taro
  • Ministan Abuja, Nyesom Wike ya kalubalanci tsohon Sanatan bayan ya yi maganganu kan yadda suka ceto dimokuraɗiyya a Najeriya

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Sanata Shehu Sani ya yi martani kan maganar da ministan Abuja Nyesom Wike ya fada a kansa yayin wani taro.

Ministan Abuja , Nyesom Wike ya kalubalanci Shehu Sani da ya nuna ayyukan cigaba da ya kawo a lokacin da yake Sanata.

Kara karanta wannan

Shehu Sani ya fadi abin da shugabannin Arewa ya kamata su mayar da hankali a kai

Shehu Sani
Shehu Sani ya yi martani ga Wike.
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Sanata Shehu Sani ya fadi wajen da yake son rama abin da ministan ya masa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shehu Sani: 'Na gano wayon Wike'

Sanata Shehu Sani ya ce a yanzu haka ya gano dabarar da Wike yake wajen zama mai magana na karshe a wuraren taro.

Shehu Sani ya ce Wike na amfani da wannar dabarar domin ya fadi abin da babu mai masa martani a wajen taro bayan ya kammala magana.

Matakin da Shehu Sani zai dauka

Shehu Sani ya bayyana cewa zai yi maganin Wike idan suka kara haduwa a wajen taro ta inda ba zai bar sa ya yi na karshe ba.

Sanatan ya kuma bayyana cewa sai sun hadu a wajen taro zai yiwa Wike maratani kan maganganun da ya fada a kansa.

Kara karanta wannan

Sanata ya yiwa Tinubu da talakawa hannunka mai sanda ganin abin da ya faru a Kenya

Shehu Sani: 'Wike na cin albarkacin mu'

Har ila yau, Sanata Shehu Sani ya ce har yanzu Nyesom Wike albarkacin yaki da mulkin soja da suka yi yake ci a Najeriya.

Ya ce da ba su yi yaki da mulkin soja ba, da Wike bai samu damar rike mukaman gwamanti ba a rayuwarsa, rahoton Channels Television.

Shehu Sani ya gargadi Tinubu

A wani rahoton, kun ji cewa Sanata Shehu Sani ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya riƙa duba cancanta wajen naɗa muƙamai a gwamnatinsa.

Tsohon sanatan na Kaduna ta Tsakiya ya gargaɗi Shugaba Tinubu kan yin irin kuskuren magabacinsa, Muhammadu Buhari wanda ya bar ofis a shekarar bara.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Online view pixel