Bayan Neman Taimako, Sanusi II Ya Gwangwaje Dattijo da Makudan Kudi a Bidiyo

Bayan Neman Taimako, Sanusi II Ya Gwangwaje Dattijo da Makudan Kudi a Bidiyo

  • Wani dattijo ya barke da murna bayan neman taimakon kudi domin lalacewar wani bangare na gidansa a Kano
  • Dattijon ya samu gudunmawar kudi har N200,000 daga Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II kan lamarin
  • An gano dattijon a cikin faifan bidiyo a fadar Sarki yana godiya tare da kora ruwan addu'o'i ga Muhammadu Sanusi II

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya taimakwa wani dattijo da makudan kudi a jihar.

Sanusi ya tallafawa dattijon da kudi N200,000 bayan ya nemi alfarma kan rushewar wani bangaren gidansa.

Sanusi II ya ba dattijo gudunmawar kudi a Kano
Muhammadu Sanusi II ya taimakawa wani dattijo da N200,000 a Kano. Hoto: @masarautarkano.
Asali: Twitter

Kano: Sanusi II ya taimaki wani dattijo

Masarautar Kano ta wallafa faifan bidiyon inda dattijon ke godiya a fada a shafin X a yau Juma'a 28 ga watan Yunin 2024.

Kara karanta wannan

Jihohi 3 da ke zargin gwamnatin tarayya da yi masu katsalandan

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sarkin ya mika wannan kyauta ce ta hannun Falakin Kano domin ya samu damar gyara bangaren gidan nasa.

Dattijon ya yi godiya ga Sanusi II

"Ina godiya sosai naga kudi, taimakon da na nema gida na ya lalace an dauki kudi har N200,000 aka bani."
"Ina matukar godiya, Allah ya raba ka da makiya ya taimake ke."

- Cewar dattijon

Daga bisani dattijon ya kora ruwan addu'o'i ga sarkin domin gudanar da mulkinsa cikin nasara ba tare da matsala ba.

Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da dambarwa kan sarautar jihar Kano tun a karshen watan Mayun 2024.

Hakan ya biyo bayan tube Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero daga sarautar tare da mayar da Muhamamdu Sanusi II kan kujerar ba tare da wani bata lokaci ba.

Masu tafsiri sun ziyarci Sanusi II

Kara karanta wannan

Sarautar Kano: Abin da Sanusi II ya fadawa kungiyar mata masu tafsiri a fadarsa

A wani labarin, kun ji cewa kungiyar mata masu tafsirin Alkur'ani mai girma ta ziyarci fadan Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II.

Kungiyar ta kai caffan ban girma domin nuna goyon baya ga sarkin inda mambobin suka kora ruwan addu'o'i ga sarkin.

Sarkin a martaninsa, ya yi musu godiya inda ya kara musu karfin guiwar ci gaba da ayyukan alheri da suke yi na Musulunci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel