Shigar Banza: An Kori Mataimakiyar Shugaban Masu Rinjaye Daga Zauren Majalisar Edo

Shigar Banza: An Kori Mataimakiyar Shugaban Masu Rinjaye Daga Zauren Majalisar Edo

  • An kwashi 'yan kallo a zauren majalisar dokokin jihar Edo a ranar Laraba, bayan da aka kori wata 'yar majalisa saboda ta yi shigar banza
  • An ruwaito cewa kakakin majalisar, Blessing Agbebaku ta umarci mataimakiyar shugaban masu rinjaye da ta fice daga zauren majalisar
  • Hon. Nicholas Asonsere ne ya gabatar da korafi gaban zauren majalisar kan shigar tsiraici da 'yar majalisar ta yi wanda ya ce ya sabawa ƙa'ida

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jihar Edo - A jiya Laraba ne aka kori mataimakiyar shugaban masu rinjaye ta majalisar Edo, Natasha Osawaru daga zauren majalisar saboda ta yi shigar banza.

Kakakin majalisar Edo, Blessing Agbebaku ta umarci Osawaru, mai wakiltar mazabar Egor da ta fice daga zauren majalisar bayan dan majalisa Nicholas Asonsere ya gabatar da korafi.

Kara karanta wannan

Manyan abubuwa sun taso a Najeriya, majalisa ta yanke hutu domin tattaunasu

Edo: An kori 'yar majalisa daga zauren majalisa saboda shigar banza
Majalisar Edo ta dauki mataki kan Natasha Osawaru da ta yi shigar banza. Hoto: Natasha Irobosa Osawaru
Asali: Facebook

'Yar majalisa ta yi shigar banza a Edo

Hon. Asonsere mai wakiltar Ikpoba-Okha ya yi nuni da cewa shigar da mataimakiyar shugaban masu rinjayen ta yi ya sabawa dokar majalisar, inji jaridar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Dan majalisar ya ce:

"Wannan zauren majalisar wani wuri ne mai tsarki wanda ba za mu amince wasu su rika yin abubuwan da basu dace ba a ciki.
"Mun jima muna kawar da kai daga wasu munanan dabi'u na 'yan majalisar mu, ya zama wajibi mu yiwa tufkar hanci tun yanzu."

"A hukunta masu karya doka" - Asonsere

Jaridar PM News ta ruwaito ɗan majalisar ya nemi izinin kakakin majalisar domin zayyana kadan daga cikin dokokin zauren majalisar.

Ya ce majalisar na da na da 'Bible' din wanda take kallo a matsayin kundin dokar gudanarwar majalisar jihar Edo.

"Duk wani mamba da ya karya dokokin da ke cikin wannan littafi, dole ne a hukunta shi bisa turbar doka."

Kara karanta wannan

Bola Tinubu zai gana da gwamnoni, za su tattauna kan mafi ƙarancin albashi a Aso Villa

- Inji Hon. Asonsere.

Majalisar dattawa ta amince da bukatar Tinubu

A wani labarin, mun ruwaito cewa majalisar dattawa ta amince da bukatar Shugaba Bola Tinubu na tsawaita wa'adin aiwatar da kasafin kudin 2023.

Majalisar ta amince za a ci gaba da amfani da kasafin 2023 tare da karin kasafin shekarar har zuwa ranar 30 ga watan Disambar 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel