Limami Ya Shiga Matsala Kan Zuwa Aikin Hajji Babu Izinin Basarake, an Yi Masa Barazana

Limami Ya Shiga Matsala Kan Zuwa Aikin Hajji Babu Izinin Basarake, an Yi Masa Barazana

  • Babban limamin masallacin Juma'a ya shiga matsala a jihar Oyo bayan tafiya aikin hajji ba tare da izinin Sarkinsa ba
  • Sarkin Ogbomosho, Oba Afolabi Ghandi ya kalubalanci limamin inda ya ce ya saba ka'idar da suka yi kafin nada shi mukamin
  • Basaraken ya ce limamin ya sanya hannu a yarjejeniya kafin nada shi mukamin wanda aka gindaya masa wasu sharuda

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Oyo - Mai sarautar Ogbomos da ke jihar Oyo, Oba Afolabi Ghandi ya nuna bacin ransa kan yadda babban limami ya saba dokarsa a yankin.

Basaraken ya caccaki babban limamin mai suna Sheikh Taliat Yunus Olusina kan tafiya aikin hajji ba tare da izininsa ba.

Kara karanta wannan

Yayin da ake rade radin tuge shi, Sultan ya tura sako ga rundunar sojoji

Basarake ya caccaki limami kan rashin masa biyayya a Oyo
Sarkin Ogbomoso, Oba Afolabi Ghandi ya kalubalanci limamin garin kan bijirewa umarninsa. Hoto: Oba Afolabi Ghandi, Taliat Yunus Olusina
Asali: Facebook

Basarake ya fusata da halin babban limami

Vanguard ta ruwaito cewa basaraken ya dade yana takun saka da limamin tsawon lokaci kafin wannan matsalar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Basaraken a cikin takardar zargin, ya ce limamin bai nemi izni ba kafin wucewa aikin hajji a Saudiyya a karan kansa.

Ya ce daukar wannan mataki na limamin ya saba yarjejeniyar da suka yi kafin a ba shi mukamin babban limami, cewar Daily Post.

Takardar da Sarki ya rubutawa limami

"Ina mai rubuta korafi a gare ka saboda wasu halaye da kake nunawa a matsayinka na limamin Ogbomoso, ya kamata ka bar irin wadannan halaye."
"Idan ba ka manta ba, kafin nada ka babban limami ka sanya hannun kan yarjejeniya da dokokin da aka gindaya maka."
"A cikin yarjejeniyar, ka sanya hannu cewa zaka sanar da sarkin Ogbomoso kafin barin kasar Najeriya zuwa wani wuri."

Kara karanta wannan

Malamin Musulunci ya kunyata 'yan siyasa a zaman makokin tsohon gwamna

- Sarki Afolabi Ghandi

Korafin basarake kan babban limami a Oyo

Basaraken har ila yau, ya kalubalanci sarkin kan nada magajinsa wanda ya jagoranci sallar Juma'a bayan tafiyarsa.

Ya ce hakan ya saba ka'idar da suka yi na cewa ba zai yi haka ba har sai da saninsa wanda ya ce dole ya zo ya amsa tambayoyi.

A martaninsa, babban limamin ya tabbatar da haka inda ya wannan ba shi ne karon farko da ya ke rubuta takarda kansa ba.

Malamin Musulunci ya shawarci 'yan siyasa

Kun ji cewa malamin Musulunci, Sheikh Muhydeen Bello ya bayyana 'yan siyasa a matsayin marasa tsoron Allah.

Shehin malamin ya shawarce su da su aikawar da ayyukan alheri lokacin da suke mulki kafin damar ta subuce musu daga baya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel