Gwamnan Kano Ya Ware N4.8bn Domin Gyara Makarantu, Mutane 17, 000 Za Su Samu Aiki

Gwamnan Kano Ya Ware N4.8bn Domin Gyara Makarantu, Mutane 17, 000 Za Su Samu Aiki

  • Gwamnatin jihar Kano karkashin gwamna Abba Kabir Yusuf ta ware makudan kudi domin yin ayyuka na musamman a ɓangare ilimi
  • Rahotanni sun nuna cewa ayyukan za su shafi dukkan kananan hukumomin jihar guda 44 domin inganta ilimin karkara da birni
  • Daraktan yada labaran gwamnatin jihar, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya yi karin haske kan ayyukan da ma'aikata da za a dauka a jihar

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Kano - Gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ware makudan kudi domin haɓaka ilimi a dukkan fadin jihar.

Gwamnatin jihar ta tabbatar da cewa manyan ayyukan za su shafi dukkan sassan jihar ciki har da ƙauyuka.

Kara karanta wannan

Ruwa ya cinye wasu dalibai a hanyarsu ta dawo wa daga jarrabawa a Kaduna

Abba Kabir
Gwamnatin Kano ta ware kudi domn inganta ilimi. Hoto: Sanusi Bature Dawakin-Tofa
Asali: Facebook

Legit ta gano haka ne cikin wani sako da daraktan yada labaran gwamnatin Kano, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya wallafa a shafinsa na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kano: Za a gyara makarantun firamare

Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya tabbatar da cewa gwamnatin ta ware N1.9b domin gyare-gyaren makarantun firamare a jihar.

Ya kuma kara da cewa kwaskwarimar za ta shafi dukkan makarantun firamare da suke kananan hukumomin jihar guda 44.

Za a gina sababbin ajujuwa a Kano

Har ila yau, Abba Kabir Yusuf ya ware kudi kimanin N2.9b domin gina ajujuwa a fadin jihar, rahoton Daily Trust.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnan ya ce za a yi amfani da kuɗin ne domin gina ajujuwa a makarantun firamare saboda inganta ilimi daga tushe.

Za a dauki ma'aikata a makarantun Kano

Har ila yau, gwamantin ta tabbatar da cewa za a ɗauki masu gadi 17,600 a makarantun jihar domin inganta tsaro.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta ware miliyoyi kan kiwon lafiya, ta yi albishir ga masu cutar sikila

An bayyana cewa kowace karamar hukuma a jihar Kano za ta samu masu gadi 400 domin kare makarantun jihar.

Gwamnatin Kano ta soke lasisin makarantu

A wani rahoton, kun ji cewa gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya soke lasisin makarantu masu zaman kansu gaba daya a jihar kwanaki.

Wannan na daga cikin matakin da gwamnati ke yi na tabbatar da makarantun sun cike tsari da ka'idoji domin samun ilimi mai inganci.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Online view pixel