Zargin Satar N432bn: El Rufai Ya Ɗauki Matakin Shari’a Kan Majalisar Dokokin Kaduna

Zargin Satar N432bn: El Rufai Ya Ɗauki Matakin Shari’a Kan Majalisar Dokokin Kaduna

  • Rahotanni sun bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya dauki matakin shari'a kan majalisar dokokin jihar
  • Malam El-Rufai ya garzaya kotu ne a ranar Laraba inda ya nemi a rusa rahoton majalisar da ya ce gwamnatinsa ta karkatar da N432bn
  • Tsohon gwamnan, wanda ya shigar da karar a kan tauye hakki ya ce majalisar Kaduna ba ta bashi damar kare kansa daga zarge zargen ba

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kaduna - Tsohon gwamna, Nasir El-Rufai ya maka majalisar Kaduna a kotu kan zarginsa da ta yi da karkatar da N432bn a shekaru takwas na mulkinsa da kuma barin dimbin bashi.

Kara karanta wannan

Bola Tinubu ya ɗauki mataki kan sabon mafi ƙarancin albashi a taron majalisar zartarwa

A ranar Larabar nan ne El-Rufai ya shigar da kara kan take 'yanci a gaban babbar kotun tarayya da ke Kaduna, inda ya ke ƙarar majalisar dokoki.

El-Rufai ya dauki matakin doka kan majalisar dokokin Kaduna
El-Rufai ya yi ƙarar majalisar dokokin Kaduna kan rahoton da ta fitar. Hoto: @elrufai
Asali: Facebook

El-Rufai ya maka majalisar Kaduna a kotu

Rahoton Channels TV ya nuna lauyan tsohon gwamnan, Abdulhakeem Mustapha SAN ne ta shigar da karar idan yake ƙalubalantar matakin majalisar na tuhumar El-Rufai da laifin 'zamba.'

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin takardar karar El-Rufai ya nemi kotun da ta rusa rahoton binciken majalisar dokokin sakamakon ba a ba shi damar kare kansa kan zarge zargen da ake yi masa ba.

Baya ga majalisar dokokin Kaduna, El-Rufai ya haɗa da Antoni janar kuma kwamishinan shari'a na jihar a cikin wadanda yake kara.

El-Rufai: Dalilin yin karar majalisar Kaduna

Mai magana da yawun tsohon gwamnan, Muyiwa Adekeye, ya wallafa a shafinsa na X cewa:

Kara karanta wannan

Abba Gida Gida zai gwangwaje manoman Kano da taki, za a kashe N5bn kan tallafi

"Malam Nasir El-Rufai ya dura babbar kotun tarayya da ke Kaduna domin rattaba hannu a karar da ya shigar kan majalisar dokokin jihar Kaduna a gaban kotun.
"El-Rufai ya je kotun ne a matsayinsa na ɗan Najeriya wanda ya ke da 'yanci a bashi damar kare kansa kafin wani kwamiti ko hukuma ta yanke hukunci kan hakkinsa.
"Bisa ga sashe na 36 na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999, El-Rufai na neman kotun ta rusa rahoton binciken basussuka, hada-hadar kudi da sauransu da majalisar ta zartar."

Majalisar ta yi kwamitin binciken El-Rufai

Tun a tsakiyar watan Afrilu ne muka ruwaito cewa majalisar dokokin jihar Kaduna ta kafa wani kwamiti da zai binciki yadda Nasir El-Rufai ya tafiyar da mulkin jihar.

Majalisar na zargin tsohon gwamnan ya karkatar da wasu kudi kuma gwamnatinsa ta ci tarin bashi ba tare da an aiwatar da wani aikin a-zo-a gani ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.