Bola Tinubu Ya Ɗauki Mataki Kan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi a Taron Majalisar Zartaswa

Bola Tinubu Ya Ɗauki Mataki Kan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi a Taron Majalisar Zartaswa

  • Majalisar zartaswa ta FEC a karkashin Bola Ahmed Tinubu ta jingine rahoton kwamitin sabon mafi ƙarancin albashi a taron yau Talata
  • Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama'a, Mohammed Idris ya ce majalisar ta yi haka ne domin bai wa Tinubu lokacin ji daga kowane ɓangare
  • Ya ce kwamitin da aka kafa kan sabon albashin ya miƙa rahotonsa amma ba zai yiwu FEC ta ɗauki mataki ba, duba da lamarin ya shafi ɓangarori da dama

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Majalisar zartaswa ta tarayya (FEC) ta jingine kundin da aka gabatar kan sabon mafi karancin albashi a taron yau Talata a Aso Villa.

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan al'umma na ƙasa, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan bayan taron majalisar a fadar gwamnatin Najeriya.

Kara karanta wannan

Bola Tinubu yana jagorantar taron FEC a fadar shugaban ƙasa, bayanai sun fito

Shugaban Kasa, Bola Tinubu.
Majalisar zartarwa ta kasa FEC ta jingine batun sabon mafi karancin albashi Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Batun mafi karancin albashi a zaman FEC

Mohammed Idris ya shaidawa masu ɗauko rahoton gidan gwamnati cewa batutuwa 39 aka gabatar a taron yau kuma majalisar ta duba su duka.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dangane da batun mafi ƙarancin albashi, ministan ya tabbatar da cewa kwamitin da aka kafa ya miƙa rahoton aikin da ya yi, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Kwamitin mafi karancin albashin da aka kafa ya ƙunshi wakilan kananan hukumomi, jihohi, kungiyoyin kwadago NLC da TUC da kuma gwamnatin tarayya.

FEC ta kara ba Bola Tinubu lokaci

Miinistan ya ce majalisar ba za ta iya yanke hukunci a kan batun ba saboda ya shafi kananan hukumomi, jihohi, kamfanoni masu zaman kansu da ƴan kwadago.

Bisa haka ne majalisar ta ga ya dace ta jingine batun domin bai wa shugaban ƙasa damar tattaunawa da jin ta bakin kowane ɓangare kafin ɗaukar matsaya.

Kara karanta wannan

NLC: Ƴan kwadago sun roki Tinubu, sun faɗi mafi ƙarancin albashin da suke buƙata

A cewarsa, Tinubu zai sake nazari kuma ya nemi shawarwari kafin ya miƙa kudirin sabon albashin ga majalisar tarayya, Channels tv ta ruwaito.

NLC ta nemi Tinubu ya ɗauki N250,000

A wani rahoton na daban kuma, ƙungiyar kwadago ta yi kira ga Bola Ahmed Tinubu ya nuna ƙaunar da yake yiwa ma'aikata ta hanyar amincewa da N250,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashi.

NLC ta bayyana cewa hakan ne kaɗai zai sa ma'aikata su samu sauƙi duba da kunci da wahalhalun rayuwar da aka shiga a ƙasar nan.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262