Dakarun Sojojin Sama Sun Yi Nasara Kan Barayin Man Fetur a Najeriya

Dakarun Sojojin Sama Sun Yi Nasara Kan Barayin Man Fetur a Najeriya

  • Rundunar sojojin saman Najeriya ta ce dakarunta sun samu nasarar kai hare-hare a haramtattun wuraren tace man fetur a yankin Kudancin Najeriya
  • A cikin wata sanarwa da daraktan hulɗa da jama'a na rundunar ya fitar, ya bayyana cewa an lalata haramtattun wuraren guda 13 da kwale-kwale guda bakwai
  • AVM Edward Gabkwet ya kuma bayyana cewa dakarun sojojin za su ci gaba da kai hare-haren har sai an ga bayan masu ɓarna ga tattalin arziƙin ƙasar nan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Rundunar sojojin saman Najeriya (NAF) ta ce dakarunta na Operation Delta Safe sun lalata haramtattun wuraren tace man fetur guda 13 da kwale-kwale bakwai a yankin Kudancin Najeriya.

Kara karanta wannan

An shiga ɗimuwa bayan wasu miyagu sun hallaka Birgediya-janar na soja a Abuja

Dakarun sojojin sun lalata haramtattun wuraren ne a jihohin Rivers, Bayelsa da Imo.

Sojojin sama sun lalata wuraren satar man fetur
Dakarun sojojin sama sun lalata wuraren satar man fetur a jihohin Imo, Bayelsa da Rivers Hoto: Nigeria Airforce
Asali: Facebook

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktan hulɗa da jama'a na rundunar sojojin sama, AVM Edward Gabkwet, ya fitar a ranar Lahadi, a birnin tarayya Abuja, cewar rahoton jaridar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda sojoji suka tarwatsa ɓarayin man fetur

Edward Gabkwet ya ce hare-haren saman da aka kai a tsakanin ranakun 18 ga watan Yuni da 22 ga watan Yuni, sun tarwatsa motocin J-5 guda biyar da ke ƙoƙarin satar man fetur daga tankoki, rahoton jaridar Leadership ya tabbatar.

Ya bayyana cewa wasu daga cikin haramtattun wuraren an gano su ne a kusa da kogin Imo a ranar 18 ga watan Yuni, inda aka lalata su yayin da masu satar man suka tsere.

Kara karanta wannan

Dakarun sojoji sun kashe ƴan bindiga 220, sun ƙwamuso wasu sama da 300 a Najeriya

A cewarsa, an kuma kai wasu hare-haren a Wilcourt a jihar Rivers a ranar, 19 ga watan Yuni, a wani haramtaccen wuri inda akwai wani kwale-kwale da ke ɗauke da kayan man fetur.

Edward Gabkwet ya kuma ƙara da cewa dakarun sojojin sun kuma lalata wasu haramtattun wuraren tace man fetur da ke a yankin Tunu cikin jihar Bayelsa.

Ya kuma ba da tabbacin cewa waɗannan hare-haren za a ci gaba da kaisu har sai an kawo ƙarshen ɓata garin.

Sojojin sama sun hallaka ƴan bindiga

A wani labarin kuma, kun ji cewa rundunar sojojin saman Najeriya ta kashe ƴan bindiga sama da 100 a wani samame da ta kai sansanin Kuka Shidda da ke karamar hukumar Faskari a jihar Katsina.

Dakarun sojojin rundunar Operation Hadarin Daji ne suka yi ruwan wuta kan ƴan bindigar da daddare, wanda bisa nasara suka murƙushe su da yawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

Online view pixel