"Matata Ta Fara Mani Wani Abu Saboda Bana Gamsar da Ita a Gadon Aure," Miji Ya Kai Ƙara Kotu
- Abin mamaki baya karewa yayin da wani magidanci ya nemi kotu ta raba aurensa saboda ba ya gamsar da matarsa a lokacin saduwa
- Dennis Sikanika ya ce matar ta ɗauki hakan a matsayin wani babban al'amari har ta fara masa barazanar kisa saboda rashin ƙoƙarinsa
- Ya shaida wa alƙalin kotun yanki cewa tun kafin a ɗaura masu aure ya faɗawa matar cewa shi rago ne a harkokin kwanciyar aure
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Zambia - Idan da ranka za ka sha kallo, wasu ma'aurata sun gurfana gaban alƙali saboda mijin ba ya iya gamsar da matar a wurin saduwar aure a kasar Zambia.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya kai ga matar ƴar kimanin shekara 32 a duniya, Faustina Chola ta fara barazanar kashe mijin matuƙar bai ƙara dagewa a gado ba.
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/5ca3c07b54231be7.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
"Yana da ɗaure kai," Falana ya faɗi kuskuren da aka yi a hukuncin shari'ar sarautar Kano
![Gudumar kotu. Gudumar kotu.](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/f09146dee624c5f9.jpg?imwidth=900)
Asali: Twitter
A rahoton da jaiƙridar Zambia Observer ta tattaro, wannan ya sa magidancin ɗan shekara 49 a duniya, Dennis Sikanika, ya maka matarsa a gaban kotu.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya roƙi ƙaramar kotun yanki da ke zamanta a Lusaka Matero, ƙasar Zambia ta taimaka ta kashe wannan aure tun kafin mai ɗakinsa ta zama ajalinsa.
Meyasa ya kai lamarin kotu?
Da yake jawabi a kotun, Mista Sinkala ya bayyana mamakinsa kan yadda matarsa ta ɗauki lamarin rashin gamsar da ita da girma har take masa barazana.
A cewarsa, ko kaɗan bai cuce ta ba domin tun kafin su yi aure a 2014 ya faɗa mata cewa shi rago ne a ɓangaren kwanciya, ba ya iya sauke nauyin namiji 100%.
Duba da wannan barazana, magidancin ya garzaya yana neman alkali ya shiga tsakani, ya raba auren kowa ya kama gabansa tun kafin ta aikata nufinta, cewar Tribune Nigeria.
![](https://netstorage-legit.akamaized.net/images/d19cf5c1089e7f84.jpg?impolicy=cropped-image&imwidth=256)
Kara karanta wannan
Kano: Gwamna Abba Kabir ya faɗi matakin da ya ɗauka kan hukuncin soke naɗin Sanusi II
Lauya ta yi wuff da mijin wata mata
A wani rahoton kun ji cewa Wata bazawara ta shiga damuwa bayan ta gano tsohon mijinta da ya sake ta ya auri lauyanta bayan gama shari'a a kotu
Lauyar ita ce ta wakilce matar a yayin da take neman saki a wajen tsohon mijinta a kotu, sannan bayan ƴan makonni ta yi wuff da shi
Asali: Legit.ng