Sarautar Kano: Abba Ya Ba Kwamishinan ’Yan Sanda Sabon Umarni Kan Fadar Nassarawa

Sarautar Kano: Abba Ya Ba Kwamishinan ’Yan Sanda Sabon Umarni Kan Fadar Nassarawa

  • Gwamnatin jihar Kano ta umarci kwamishinan 'yan sanda ya fitar da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado daga fadar Nasarawa
  • Abba Kabir Yusuf ya ba da wannan umarni domin fara gyara a wasu bangarori na fadar da ke Kano ba tare da bata lokaci ba
  • Wannan na zuwa ne awanni kadan bayan hukuncin Babbar Kotun Tarayya kan rigimar masarautun jihar da ake ta yi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Gwamna Abba Kabir ya umarci fitar da sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero daga fadar Nasarawa a jihar Kano.

Abba Kabir ya ba da umarnin ne ga kwamishinan 'yan sanda a jihar, Hussaini Gumel inda ya ce zai yi gyara tare da rushe-rushe.

Kara karanta wannan

Hukuncin masarautar Kano ya lasawa bangarorin da ke rikici zuma a baki

Abba Kabir ya umarci rushe fadar Aminu Ado a Kano
Gwamna Abba Kabir ya umarci fitar da Aminu Ado Bayero daga fadar Nasarawa. Hoto: @Kyusufabba, @masarautarkano.
Asali: Twitter

Kano: Umarnin Abba game da fadar Nasarawa

Kwamishinan shari'ar a jihar, Haruna Isa Dederi shi ya fitar da wannan sanarwa yayin ganawa da manema labarai, cewar TVC News.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dederi ya ce gwamnatin jihar ta gama shirin rushewa tare da gyara na musamman a katangun fadar da suka mutu, Daily Trust ta tattaro.

"Wannan hukunci na kotu ya tabbatar da dokar Majalisar jihar da Gwamna Abba Kabir ya sanyawa hannu a ranar 23 ga watan Mayun 2024."
"Bayan haka, gwamnatin jihar Kano ta umarci kwamishinan 'yan sanda ya fitar da Aminu Ado inda aka shirya fara gyara a fadar tare da rushe wani bangare na katangar ba tare da bata lokaci ba."

- Haruna Isa Dederi

Masarautun Kano: Kotu ta yi hukunci

Wannan sanarwa na zuwa ne awanni kadan bayan Babbar Kotun Tarayya ta yi hukunci kan rigimar sarautar Kano.

Kara karanta wannan

Soke naɗin Sanusi II: Gwamnatin Kano ta yi martani kan hukuncin da kotu ta yanke

Kotun ta yi fatali da matakan da matakan da gwamnan jihar ya dauka wajen aiwatar da rushe masarautun.

Yan Najeriya sun yi martani hukuncin kotu

A wani labarin, kun ji cewa bayan hukuncin kotu a yau Alhamis 20 ga watan Yunin 2024 kan dambarwar sarautar Kano.

Kotun yayin hukuncin ta rushe matakin da Gwamna Abba Kabir ya dauka kan soke masarautun jihar guda biyar.

Mutane da dama sun yi martani inda suka bayyana ra'ayoyinsu mabambanta gamed da hukucin da kotun ta yanke.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel