Sanusi II Vs Aminu: Babbar Kotu Za Ta Yanke Hukunci a Shari'ar Sarautar Kano

Sanusi II Vs Aminu: Babbar Kotu Za Ta Yanke Hukunci a Shari'ar Sarautar Kano

  • Babbar kotun tarayya za ta yanke hukunci kan ko tana da hurumin sauraron shari'ar sarautar Kano yau Alhamis, 13 ga watan Yuni
  • Aminu Babba Ɗanagundi ne ya kai ƙara gaban kotun yana ƙalubalantar matakin gwamnatin Kano na mayar da Muhammadu Sanusi II
  • A zaman shari'ar, lauyoyi sun gwabza kan hurumin kotun wanda a ƙarshe aka tsara yanke hukunci yau Alhamis, 13 ga watan Yuni

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - A yau Alhamis, 13 ga watan Yuni, babbar kotun tarayya mai zama a Kano za ta yanke hukunci kan ko tana da hurumin sauraron kara kan rigimar sarautar Kano.

Idan ba ku manta ba gwamnatin Kano karkashin jagoancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta mayar da Muhammadu Sanusi II kan sarauta a matsayin sarki na 16.

Kara karanta wannan

"Ka bi sawun kakanka," Iyalan Sheikh Ibrahim Nyass sun aike da saƙo ga Sanusi II

Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero.
Yau kotun tarayya za ta sanar da hukuncinta kan hurumin sauraron shari'ar sarautar Kano Hoto: @ImranMuhdz
Asali: Twitter

Dalilin shigar da kara kan sarautar Kano

Rahoton Leadership ya ce Aminu Babba Danagundi, daya daga cikin dattawan masarautar Kano da aka tube ya maka gwamnatin Kano a gaban kotun yana neman haƙƙinsa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ɗanagundi ya roƙi kotun ta dawo masa da haƙƙinsa wanda yake zargin gwamnatin Kano ta take a lokacin da ta tsige shi daga sarautar Sarkin Dawaki Babba.

Lauyoyi sun yi muhawara sosai kan hurumin kotun tarayya a batun da ya shafi dokar da ta tsige Aminu Bayero a matsayin Sarkin Kano na 14.

Lauyoyin sun gwabza a shari'ar sarauta

Barista M. A. Waziri, lauyan wanda ya shigar da kara, Aminu Danagundi da aka tsige daga Sarkin Dawaki Babba, ya ce kotu na da cikakken hurumin sauraren karar.

Ya kuma kara da cewa ba a yi wa wanda yake karewa adalci ba kafin a tsige shi, don haka an tauye masa hakki, kuma tsarin da aka bi na dawo da Sarki Sanusi II ya saɓa doka.

Kara karanta wannan

Sanusi II Vs Aminu: An kawo cikas a zaman shari'ar masarautar Kano ana shirin sallah

A ɗaya bangaren, lauyan Sanusi II, Barista Muhmud A. Magaji, ya bukaci kotun da ta yi watsi da duk bayanin mai kara na cewa tana da hurumin ci gaba da shari’ar.

Ya kara da cewa babu shakka majalisar dokokin jihar tana da hurumin gyara, soke ko ma samar da wata doka da ta dace da jihar, rahoton Vanguard.

A ƙarshe dai kotun ta ɗage zaman zuwa yau Alhamis domin yanke hukunci kan ko tana da hurumin sauraron shari'ar rikicin sarautar da ke faruwa a Kano.

Yan daba sun tada hargitsi a Kano

A wani rahoton kuma Ƴan daba sun tayar da hargitsi a kasuwar da ke Masallacin idi a Kano bayan gwamnatin jihar ta umarci mutane su tashi.

Gwamnatin Kano ta bai wa ƴan kasuwar wa'adin sa'o'i 48 su tashi daga wurin, amma har yanzu ana ci gaba da hada-hada.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel