Goodluck Jonathan Ya Bayyana Nasara 1 da Najeriya Ta Samu Saboda Dimokuraɗiyya

Goodluck Jonathan Ya Bayyana Nasara 1 da Najeriya Ta Samu Saboda Dimokuraɗiyya

  • Tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan ya yi jawabi kan cikar Najeriya shekaru 25 kan turbar dimokuraɗiyya
  • Shugaba Goodluck Jonathan ya kuma yi karin haske kan yadda lamura ke tafiya a Najeriya duk da tarin matsalolin ƙasar
  • An ruwaito cewa tsohon shugaban kasar ya yi jawabin ne a fadar sarkin Benin yayin wata ziyara da ya kai a jiya Talata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Edo - Yayin da ake cika shekaru 25 da dorewar mulkin dimokuraɗiyya a Najeriya, tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya yi bayani.

Shugaba Jonathan ya ce duk da tarin matsalolin da ake fama da su a Najeriya, akwai abin da za ta yi alfahari da shi.

Kara karanta wannan

'Gina Legas': Sule Lamido ya ragargaji Tinubu, ya fadi yadda PDP za ta ceto Najeriya

Jonathan
Goodluck Jonathan ya bukaci a cigaba da bin tsarin dimokradiyya. Hoto: Goodluck Ebele Jonathan
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa shugaban ya yi jawabin ne jim kaɗan bayan ganawa da Oba Ewuare II a fadarsa da ke Benin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jonathan: "Najeriya ta samu ribar dimokuraɗiyya"

A yayin da yake hira da yan jarida, shugaba Goodluck Jonathan ya ce har yanzu a Najeriya mutane suna da damar tofa albarkacin baki kan lamuran kasar.

Goodluck Jonathan ya ce hakan abin alfahari ne ga yan kasa kasancewar a baya, lokacin mulkin soja, ba haka lamarin yake ba.

A cigaba da bin dimokradiyya

Har ila yau shugaba Goodluck Jonathan ya ce ka da yan Najeriya su yi tsammanin magance matsalolin ƙasar a kankanin lokaci, rahoton Tribune.

Jonathan ya ce gyara abu ne da ke ɗaukan lokaci mai tsawo kafin a cimma shi, saboda haka a cigaba da ƙoƙarin tafiya kan tsarin dimokuraɗiyyar har a kai inda ake so.

Kara karanta wannan

Jonathan ya bayyana abu 1 da zai hana 'yan siyasa zuwa kotu idan sun fadi zabe

Oba Ewuare II ya godewa Jonathan

Goodluck Jonathan ya je Benin ne domin ƙaddamar da wani taro da zai jagoranta a jihar Edo sai ya garzaya fada domin neman albarkar sarki.

Saboda haka Oba Ewuare II ya mika godiya ga tsohon shugaban kasar bisa girmama fadar da yake yi a kowane lokaci.

Gwamnati ta ba da hutun dimokradiyya

A wani rahoton, kun ji cewa ministan harkokin cikin gida, Hon. Olubunmi Tunji-Ojo ya ayyana ranar Laraba 12 ga watan Yuni a matsayin ranar hutu ga 'yan Najeriya.

Rahotanni sun nuna cewa 12 ga watan Yuni na kowace shekara gwamnatin tarayya ta tsayar domin yin bikin murnar zagayowar ranar dimokuradiyyar Najeriya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng