Gwamnatin Abba Kabir Yusuf Ta Dauki Matakan Inganta Ilimi a Kano
- Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta dauki sabon mataki domin farfaɗo da darajar ilimi a jihar
- Gwamna Abba ya ce bangaren ilimi yana buƙatar kulawa ta musamman a jihar Kano musamman abin da ya shafi malamai
- Sabon matakin da gwamnatin jihar ta dauka ya biyo bayan dokar ta ɓaci da gwamnan ya saka a kan harkar ilimi ne a jiya Asabar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Kano - Gwamnan jihar Kano, injiniya Abba Kabir Yusuf ya dauki matakin samar da karin malamai da dakunan bincike a jihar.
Gwamnan ya ce ya dauki matakin ne domin ganin ilimi ya inganta da kuma ganin jihar ta yi fice tsakanin sauran jihohin Najeriya.

Asali: Facebook
Legit ta tabbatar lamarin ne cikin wani sako da mai taimakawa gwamnan jihar kan harkokin sadarwa, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya wallafa a shafin Facebook.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Matsalar ilimi a Kano
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da samuwar tarin matsaloli a harkar ilimi a jihar ciki har da ƙarancin kwararrun malamai.
Abba Kabir Yusuf ya kara da cewa akwai ƙarancin samun horo akai-akai ga malamai da kuma rashin abubuwa na musamman kamar ruwa da banɗaki a makarantu.
Abba zai dauki malamai a Kano
Saboda rage matsalolin ilimi, gwamna Abba ya ce zai dauki malamai 10,000 da za a rika ba su horo domin ganin sun samu kwarewa kan aikin koyarwa.
Har ila yau ya kara da cewa za a dauki ma'aikata 1,000 a manyan makarantun jihar domin inganta ilimin gaba da sakandare.
Za a gina dakunan bincike a Kano
Wani karin mataki da gwamnan ya dauka shi ne cewa zai samar da ɗakunan bincike 300 a makarantu 100 da ke fadin jihar.
Ya ce hakan zai rika ba dalibai damar samun yin bincike mai zurfi da inganci da kuma kawo cigaba a jihar Kano da kasa baki daya.
A karshe gwamnan ya ce saboda rage cinkoson dalibai zai samar da karin ajijuwa 1000 a fadin jihar.
Yan adawa sun saka Abba a gaba
A wani rahoton, kun ji cewa tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso ya magantu kan irin kokarin 'yan adawa na kawo rudani a jihar a mulkin Abba Kabir.
Kwankwaso ya zargi jam’iyyun adawa da neman dagula jihar bayan kammala zaben inda suka shiga kotu domin kalubalantar zaben.
Asali: Legit.ng