Katsina: Gwamna Ya Ba Ma’aikata Goron Sallah N45,000, Ya Gindaya Sharuda

Katsina: Gwamna Ya Ba Ma’aikata Goron Sallah N45,000, Ya Gindaya Sharuda

  • Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya ba ma’aikatan jihar kyautar N15,000 da bashin N30,000 domin bikin sallah
  • Gwamnan ya ce ma’aikatan za su biya N30,000 cikin watanni uku da za a fara cirewa daga watan Yuli mai kamawa
  • Wannan matakin gwamnan na zuwa ne yayin ake shirye-shiryen gudanar da bikin babbar salla a fadin duniya baki daya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Katsina – Gwamna Umaru Dikko Radda na jihar Katsina ya gwangwaje ma’aikata da barka da sallah a jihar.

Radda ya ba da kyautar N15,000 ga duka ma’aikatan jihar yayin da kuma ya ba su bashin N30,000 domin gudanar da salla cikin walwala.

Kara karanta wannan

"Jima'i kadai ke rage mana kunci": 'Yan gudun hijira sun cika sansani da jarirai

Radda ya ba ma'aikatan jihar Katsina goron sallah
Gwamna Dikko Umar Radda ya gwangwaje ma'aikata da kyutar kudi na goron sallah. Hoto: Dikko Umaru Radda.
Asali: Twitter

Katsina: Radda ya ba ma'aikata goron sallah

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da gwamnan ya wallafa a shafinsa na X a yau Asabar 8 ga watan Yuni.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnan ya ce ya dauki wannan matakin ne domin ragewa ma’aikatan jihar halin da ake ciki a fadin kasar.

Katsina: Yadda ma'aikata za su biya kudin

“Ganin yadda babbar sallah ke karatowa, na dauki matakin tallafawa ma’aikata wurin ba su bashin N45,000 hade da goron sallah.”
“Domin saukaka musu biyan kudin cikin sauki, za a cire N10,000 kowane wata har N30,000 a watannin Yuli da Agusta da kuma Satumba.”
“Sannan na ba duka ma’aikatan jihar kyautar N15,000 domin gudanar da bukuwan sallah cikin walwala.”

Dikko Umaru Radda

Gwamnan ya ce hakan zai yi matukar tallafawa ma'aikatan jihar gudanar da bukukuwan sallah cikin walwala.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da shari'ar sarautar Kano, Abba ya biya wa ɗalibai 119,903 kudin NECO

Katsina: Radda ya magantu kan matsalar tsaro

A wani labarin, kun ji cewa Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya yi magana kan hanyar magance matsalar rashin tsaro da ta addabi ƙasar nan.

Gwamnan ya jaddada buƙatar gwamnati ta mamaye tare da rage wuraren da ba su ƙarƙashin ikonta.

Ya kuma nuna buƙatar magance matsalar iyakokin ƙasar nan tare da kawo ƙarshen cin hanci da rashawa, inda ya ce hakan zai taimaka matuƙa wajen magance matsalar rashin tsaro a ƙasar nan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.