“Za a Tuna da Kai”: Tinubu Ya Karrama Babban Marubucin Najeriya, Wole Soyinka

“Za a Tuna da Kai”: Tinubu Ya Karrama Babban Marubucin Najeriya, Wole Soyinka

  • Shugaba Bola Tinubu ya karrama babban marubucin Najeriya, Wole Soyinka ta hanyar sanya wa sabuwar hanyar N20 sunan sa
  • An kaddamar da titin N20 da ya taso daga 'Northern Parkway' zuwa wajen sha tale-talen arewacin Abuja (ONEX) a ranar Talata
  • Tinubu ya kambama Farfesa Wole Soyinka wanda ya ce ya jawo wa Najeriya farin jini, da kuma samun tarin yabo a duniya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Shugaba Bola Tinubu ya sanya wa sabuwar hanyar N20 da aka kaddamar a Abuja sunan Farfesa Wole Soyinka domin karrama babban marubucin kasar.

Tinubu ya karrama Wole Soyinka
Tinubu ya sanya wa titin N20 na Abuja sunan Wole Soyinka. Hoto: @officialABAT, @WSoyinkaCentre
Asali: UGC

Shugaban kasar ya kaddamar da titin da ya taso daga 'Northern Parkway' zuwa wajen sha tale-talen arewacin Abuja (ONEX) a ranar Talata.

Kara karanta wannan

Yajin aikin kungiyoyin ƙwadago ya ɗauki zafi, an rufe ofishin ministan Abuja

Bola Tinubu ya bugi kirji da titin N20

Titin na N20 na daya daga cikin manyan hanyoyin da suka hada da ONEX da wajen sha tale-talen kudancin Abuja (OSEX) ta hanyoyi shiga daban-daban, in ji rahoton Channels.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale, hanyar za ta inganta zirga-zirgar ababen hawa daga gundumomin Mabushi, Katampe, Jahi, da Kado.

Jaridar The Nation ta ruwaito Tinubu ya bayyana aikin hanyar a matsayin wata shaida ta nuna nasarar gwamnatinsa na kawo sauyi a kowane bangare na kasar nan.

Tinubu ya karrama Wole Soyinka

Shugaban kasar a lokacin da yake jawabi a wajen taron kaddamar da titin ya bayyana sunan titin na N20 a matsayin 'hanyar Wole Soyinka'.

Shugaba Tinubu ya ce:

“Bari in ce shawarar sanya sunan wannan titin na N20 a matsayin 'hanyar Wole Soyinka' ta samu karbuwa sosai. Shi ne babban marubucinmu, kuma wanda ya ci kyautar 'Nobel'.

Kara karanta wannan

An jero manyan nasarori 7 da Tinubu ya samu a kwana 365 da ya canji Buhari

“Ya jawo wa Najeriya farin jini, da kuma samun tarin yabo a duniya wanda ba za a manta da shi ba.Mun yarda da wannan shawarar a madadin al'ummar tarayyar Najeriya."

Kaduna: Amarya ta datse mazakutar ango

A wani labarin, mun ruwaito cewa wata amarya, Habiba Ibrahim ta datse mazakutar angonta Salisu Idris yana barci a garin Kudan da ke jihar Kaduna.

Salisu ya bayyana kaduwarsa kan wannan mummunar aika-aika da Habiba ta yi masa yana mai cewa babu wani sabani da ya shiga tsakaninsu a iya saninsa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel