Kano: Yadda Sarki Sanusi II da Aminu Ado Bayero Suka Yi Sallar Jumu'a a Masallatai 2

Kano: Yadda Sarki Sanusi II da Aminu Ado Bayero Suka Yi Sallar Jumu'a a Masallatai 2

  • Hankali ya kwanta yayin da Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero suka yi Jumu'a a masallatai daban-daban a Kano
  • Sarki Sanusi II ya jagoranci sallah a babban masallacin Ƙofar Kudu yayin da Aminu Bayero ya yi Jumu'a a ƙaramar fadar Nasarawa
  • Tun farko dai rundunar ƴan sanda ta musanta raɗe-raɗin da ke yawo cewa dukkan sarakunan zasu yi Jumu'a a masallacin Ƙofar Kudu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero sun yi sallar Jumu'a a wurare daban-daban yau 31 ga watan Mayu, 2024.

Sanusi II ya jagoranci magoya bayansa a babban masallacin fadar Ƙofar Kudu, inda ya yi limancin sallar Jumu'a.

Kara karanta wannan

Masarautar Kano: Aminu Bayero zai jagoranci sallar Juma'a? 'Yan sanda sun magantu

Muhammadu Sanusi da Aminu Ado Bayero.
Hankula sun kwanta yayin da Sarki Sanusi da Aminu Ado Bayero suka yi Sallaha masallatai daban-daban Hoto: @masarautarkano
Asali: Facebook

Sanusi II da Aminu sun yi Juma'a

A ɗaya ɓangaren kuma sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero ya yi Jumu'a tare da magoya bayansa a gidan sarki da ke Nasarawa, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tun farko dai magoya bayan sarakunan sun fara yaɗa jita-jitar cewa Sanusi II da Aminu sun shirya gudanar da sallar Jumu'a a babban masallacin fadar sarki.

Wannan lamari dai ya jefa tsoro da fargaba a zuƙatan mazauna Kano saboda gudun abin da ka iya zuwa ya dawo idan sarakunan suka haɗu a wuri ɗaya.

Hankula sun kwanta a garin Kano

Sai dai kuma daga baya, sarakunan sun nuna cewa kowanen su zai yi sallah a masallaci daban, lamarin da ya sa aka samu kwanciyar hankali a tsakanin Kanawa.

Daga ƙarshe dai Sarki Sanusi II ya yi limancin Jumu'a a babban masallacin Ƙofar Kudu yayin da Aminu Bayero ya yi sallah a ƙaramar fadar Nasarawa.

Kara karanta wannan

Kano: Tashin hankali yayin da Sarki Sanusi II da Aminu Ado ke shirin sallar Jumu'a

Tuni dai kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Mohammed Gumel, ya karyata rade-radin da ake yaɗawa na cewa Aminu Bayero zai yi sallar Juma’a a fadar da Sanusi ke ciki.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna ya fitar, CP Gumel ya bayyana rade-radin a matsayin karya, Tribune Nigeria ta ruwaito.

“Rundunar ‘yan sanda na kira ga jama’a da su yi watsi da labaran karya da ake yadawa a soshiyal midiya cewa Sarki Alhaji Aminu Ado Bayero zai jagoranci Sallar Juma’a a babban masallacin Kofar Kudu."

Gwamnan Kano ya gana da Nuhu Ribaɗu

A wani rahoton kuma Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ziyarci Nuhu Ribado yayin da ake ci gaba da dambarwar masarautar Kano.

Darakta janar ga gwamna Abba kan yada labarai, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya ce shugabannin biyu sun tattauna batutuwan da suka jibanci ci gaban kasa da jiha.

Kara karanta wannan

Sanusi II vs Aminu: 'Yan majalisan Kano 12 sun yi mubaya'a ga Sarki na 15

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel