Kungiyar Yarbawa Ta Caccaki Salon Mulkin Tinubu, Ta Kawo Masa Mafita

Kungiyar Yarbawa Ta Caccaki Salon Mulkin Tinubu, Ta Kawo Masa Mafita

  • Ƙungiyar Yarbawa ta Afenifere ta yi magana kan shekara ɗaya da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya kwashe yana mulkin Najeriya
  • Ƙungiyar ta caccaki manufofin shugaban ƙasan kan tattalin arziƙin inda ta ce ya jefa ƴan Najeriya cikin halin talauci da tsadar rayuwa
  • Afenifere ta buƙaci Shugaba Tinubu ya janye tsarin gwamnatinsa na janye tallafin fetur da yawan jibga haraji da yake yi kan ƴan Najeriya

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Ƙungiyar Yarbawa ta Afenifere ta buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sake duba manufofinsa kan tattalin arziƙin ƙasar nan.

Ƙungiyar ta yi nuni da cewa manufofin shugaban ƙasar nan kan tattalin arziƙi sun jefa ƴan Najeriya cikin talauci.

Kara karanta wannan

Kungiyar sarakuna ta ba Sanusi II shawara kan rikicin masarautar Kano

Afenifere ta caccaki manufofin gwamnatin Tinubu
Kungiyar Afenifere ta ce Tinubu ya jefa 'yan Najeriya cikin talauci Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren ƙungiyar, Justice Faloye ya fitar, cewar rahoton jaridar Vanguard.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Afenifere ta caccaki manufofin Tinubu

Ƙungiyar Afenifere ta caccaki manufofin Shugaba Tinubu kan tattalin arziƙi.

Afenifere tayi nuni da cewa abubuwa sun ƙara taɓarɓarewa fiye da lokacin gwamnatin da ta gabace shi, rahoton jaridar The Punch ya tabbatar.

Ƙungiyar ta bayyana cewa a cikin shekara ɗaya ta gwamnatin Tinubu, tattalin arziƙin ƙasar nan ya shiga halin ƙaƙaniƙayi fiye da lokacin gwamnatin baya.

Ƙungiyar ta kuma caccaki cire tallafin man fetur da mayar da farashin canjin kuɗi na bai ɗaya, inda ta ce waɗannan matakan sun taimaka wajen taɓarɓarewar tattalin arziƙi da jefa ƴan Najeriya cikin wuya.

Wace mafita ƙungiyar ta kawowa Tinubu?

Ƙungiyar ta yi kira ga gwamnati da ta fahimci tattalin arziƙin ƙasar nan ta yadda za ta rage hauhawar farashin kayayyaki, rashin aikin yi, rashin matsuguni da talaucin da ake fama da shi.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta dawo da shirin rage talauci ga 'yan Najeriya miliyan 75

Ta buƙaci gwamnati da ta janye tsarin cire tallafin man fetur da yawan jibga haraji kan ƴan Najeriya.

Ta yi nuni da cewa waɗannan manufofin sun taimaka wajen taɓarɓarewar tattalin arziƙi wanda hakan ya jawo hauhawar farashin kayayyaki da raguwar kuɗaɗen shiga da mutane ke samu.

Tinubu ya rattaɓa hannu kan sabon ƙudiri

A wani labarin kuma, kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya rattaba hannu a kan kudirin dokar taken Najeriya da majalisar dokokin tarayya ta zartar.

Rattaɓa hannun da shugaban ƙasan ya yi kan sabon ƙudirin ya sanya za a dawo da yin amfani da tsohon taken Najeriya na “Najeriya, mun jinjina miki”.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

Online view pixel