Kungiyar Arewa ta Roki Sarkin Kano 15 Aminu Ado Bayero ya Rungumi Kaddara

Kungiyar Arewa ta Roki Sarkin Kano 15 Aminu Ado Bayero ya Rungumi Kaddara

  • Kungiyar kwararru a Arewa ta NPF ta roki sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero kan ya karbi kaddarar cire shi daga sarauta da gwamnati ta yi
  • Darakta Janar a kungiyar Usman Yusuf ne ya yi rokon ta cikin sanarwar da kungiyar ta fitar, inda ya ce sarkin na 15 ya yi hakuri shi zai fi
  • Har yanzu ana dambarwar masarautar Kano domin Sarki Aminu Ado Bayero har yanzu yana jihar tare da zaman fada a gidan Sarki a Nassarawa

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano - Kungiyar kwararrun ma'aikata a Arewacin Najeriya (NPF) ta roki Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero ya rungumi kaddara kan sauke shi da gwamnati ta yi.

Kara karanta wannan

Aminu Ado: Dalilin kotu na umartar jami'an tsaro su fitar da Sarkin Kano na 15 daga fada

A makon da ya gabata ne gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta rushe masarautun jihar biyar tare da nada sabon sarki.

Sarki
Kungiyar Arewa ta roki sarki Aminu Ado Bayero ya hakura da sarautar Kano Hoto: Hoto: masarautarbichi, sanusilamidoofficial
Asali: Facebook

A sanarwar da kungiyar ta fitar, ta ce akwai bukatar tabbatar da zaman lafiya saboda haka ta roki sarkin ya hakura, kamar yadda Nigerian Tribune ta wallafa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

NPF: A yiwa Sarki Sanusi II mubayawa

Kungiyar kwararrun ta Arewacin kasar nan, ta nemi 'yan siyasa da sauran jama'a su yiwa Sarki Muhammadu Sunusi II mubayawa.

A sanarwar da kungiyar ta fitar dauke da sa hannun darakta janar dinta, Usman Yusuf, ta bukaci a tabbatar da zaman lafiya.

Usman Yusuf ya kara da cewa kamata ya yi Sarki na 15 ya nuna dattako wajen rungumar lamarin a matsayin kaddara.

Masarauta: Jigon APC ya nemi taimakon Tinubu

Daya daga magoya bayan tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, Alhaji Abdul-Majid Danbilki Kwamanda ya roki shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tsoma baki cikin dambarwar masarautar Kano.

Kara karanta wannan

Rikicin Kano: Abin da Sarki Sanusi II ya faɗawa manyan jami'an tsaro a fadarsa

Vanguard News ta wallafa cewa Danbilki kwamanda na ganin bai kamata gwamnatin Tinubu ta rufe idanu har gwamnatin Kano ta tsige sarakuna ta nada sabo ba duk da umarnin kotu.

Gaskiya ta bayyana kan dawowar Aminu Ado

A baya mun kawo muku labarin yadda sarkin Dawaki, Aminu Babba Danagundi ya bayyana yadda aka dawo da sarkin kano na 15, Aminu Ado Bayero.

Ya musanta zargin cewa ofishin mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro karkashin Nuhu Ribadu ne ya bayar da jiragen dawo da shi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.

Online view pixel