Sarki Sanusi II Ya Dawo Gida, Ya Isa Fadar Gwamnatin Kano a Shirin Komawa Sarauta

Sarki Sanusi II Ya Dawo Gida, Ya Isa Fadar Gwamnatin Kano a Shirin Komawa Sarauta

  • Rahotanni sun nuna cewa Sarki Muhammadu Sanusi II ya isa gidan gwamnatin jihar Kano da safiyar ranar Jumu'a, 24 ga watan Mayu, 2024
  • Sarkin zai karɓi takadar mayar da shi kan kujerar sarautar Kano daga hannun Gwamna Abba Kabir Yusuf sannan ya wuce fadar Nasarawa
  • Ana sa ran Sarki Sanusi zai halarci taron hawan doki a gidan gwamnati kuma zai jagoranci sallar Jumu'a a babban masallaci da ke fadar Ƙofar Kudu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II ya isa fadar gwamnatin jihar domin karɓar takardar shaidar dawowarsa kan karagar sarauta.

A yau Jumu'a, Gwamna Abba Kabir Yusuf zai miƙa wa Sarki Sanusi II takardar shaidar mayar da shi kan kujerar sarauta ɗaya tilo mai daraja a jihar Kano.

Kara karanta wannan

Sarkin Kano: Duk da umarnin kotu, Gwamna Abba zai mika takardar nadi ga Sanusi II

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi.
Sarki Muhammadu Sanusi ya isa gidan gwamnatin Kano da safiyar Jumu'a Hoto: Masarautar Kano
Asali: Facebook

An tattaro cewa Sarkin ya koma Kano da yammacin ranar Alhamis kuma an shirya masa ƙaramar liyafar maraba da zuwa gida saboda shawarwarin tsaro.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, zuwa yanzu an kammala duk wasu shirye-shirye na sake fitowar Sanusi II a matsayin Sarki karon farko bayan mayar da shi a sarauta.

Ana sa ran Sarki Sanusi zai je ɗakin taron Africa House da ke cikin gidan gwamnatin Kano domin halartar hawan dawaki na murnar dawowarsa da misalin ƙarfe 10:00 na safe

Sarki Sanusi zai shiga fada yau

Daga nan kuma zai wuce fadar mai martaba Sarkin Kano da ke Nasarawa a cikin ƙwaryar birni.

Bayan haka ne Mai Martaba Sarki Sanusi zai wuce zuwa babban masallacin Kano da ke fadar Ƙofar Kudu domin jagorantar sallar Jumu'a yau 24 ga watan Mayu, 2024.

Kara karanta wannan

Kotu ta dakatar da gwamnatin Kano daga mayar da Sanusi II gidan sarauta

A ranar Alhamis ne Gwamna Abba Yusuf ya sake nada Sanusi a matsayin Sarkin Kano, shekaru hudu bayan tsohon gwamnan jihar Abdullahi Ganduje ya tsige shi.

Bugu da kari, gwamnan ya sauke sarakuna biyar da Ganduje ya nada tare da ba su wa'adin sa'o'i 48 da su bar masarautunsu, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Abubuwa 7 game da Sanusi

Legit Hausa ta tattaro maku wasu muhimman abubuwa da ya kamata ku sani game da Sarkin Kano na 14 a tarihi, Muhammadu Sanusi na II.

Idan za ku iya tunawa a 2020, tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya sauke Sarki Sanusi II kuma ya maye gurbinsa da Alhaji Aminu Ado Bayero.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel