Ramadan 2024: Muslman Najeriya Na Zuba Ido Kan Ganin Jaririn Watan Ramadana

Ramadan 2024: Muslman Najeriya Na Zuba Ido Kan Ganin Jaririn Watan Ramadana

  • Ana ci gaba da jiran ganin watan Ramadana ko sabanin haka a Najeriya, yayin da aka gani a wasu kasashen duniya
  • Kasar Saudiyya ta sanar da ganin jaririn watan Ramadana, za a fara Azumi a ranar Litin 11 ga watan Maris
  • Ya zuwa yanzu dai, hukumomin ganin wata a Najeriya daga fadar sarkin Musulmi sun ce a ci gaba da duban watan mai alfarma

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Salisu Ibrahim ne babban editan sashen Hausa na Legit. Kwararren marubucin fasaha, harkar kudi da al'amuran yau da kullum ne, yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru takwa

Najeriya - Al’ummar Najeriya da sauran kasashen duniya na ci gaba da zuba ido kan ganin watan Ramadana domin fara ibada mafi girma a wurin Musulmai.

Ya zuwa yanzu, ana ci gaba da shiri da sanya ido a kasar domin samun rahotannin da ke bayyana ganin watan ko akasin hakan.

Kara karanta wannan

Ramadan 2024: Jerin kasashen da musulmai za su yi azumi mafi tsawo da gajarta

Ana ci gaba da duban wata a Najeriya
Ana ci gaba da duban watan Ramadana a Najeriya | Hoto: GettyImages, moonsightingng (X)
Asali: UGC

A lissafin wata, yau ne 29 ga watan Sha’aban, wacce ke zuwa gabanin Ramadana da ake Azumin kwanaki 29 ko 30.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Me ake yi a watan Ramadana?

Watan Ramadana ne na tara a jerin watannin Muslunci 12, kuma a ciki ne Musulmai ke ba da himma ga aikata ayyukan ibada, musamman yawaita sallah da Azumi.

Wannan lamari ne da ke daukar hankalin duniya, domin duk Musulmi yake a duniya kan azumci wannan wata mafi shahara a addinin Islama.

Ana kwadaitar da Musulmai su kasance masu kamewa da yawaita neman gafara da rokon ni’imomin Allah a cikin watan.

An ga wata a kasar Saudiyya

A gobe Litinin 11 ga watan Maris ne za a fara Azumin watan Ramadana a kasar Saudiyya.

Wannan na zuwa ne bayan sanar da ganin watan a yammacin yau Lahadi, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Kara karanta wannan

Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya buƙaci a fara duba jinjirin watan azumin Ramadan 1445H

A wasu lokutan, akan saba tsakanin Najeriya da Saudiyya wajen daukar Azumi da kuma ajiye shi a watan Ramadana.

Sarkin Musulmi ya umarci a fara duban wata

A tun farko, mai alfarma sarkin musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya umarci ɗaukacin al'ummar Musulmi a Najeriya su fara duba jinjirin watan Ramadan daga ranar Lahadi.

Majalisar koli ta shari'ar musulunci a Najeriya (NSCIA) karkashin Sarkin Musulmi ce ta nemi a fara duba watan a wata sanarwa ranar Jumu'a.

Sanarwan mai ɗauke da sa hannun Farfesa Salisu Shehu, majalisar ta nemi a fara duba jinjirin watan Ramadan ranar Lahadi wanda ya zo daidai da 29 ga watan Sha'aban, 1445H.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.