Tashin Hankali: Mummunan Rikici Ya Ɓarke a Jami'ar Tarayya, An Kashe Ɗalibi Tare da Jikkata Wasu
- Sabon rikici mai alaka da ƙungiyoyin asiri ya ɓarke a jami'ar fasaha ta tarayya da ke birnin Owerri (FUTO) da safiyar ranar Jumu'a, 1 ga watan Maris
- Rahotanni sun nuna cewa an kashe ɗalibin FUTO ɗaya tare da jikkata wasu da dama yayin da suka yi faɗa da ɗaliban jami'an jihar Imo
- Legit Hausa ta fahimci cewa ɗaliban jami'ar IMSU ne suka kutsa kai cikin FUTO, lamarin da ya kawo tashin rikici a tsakaninsu
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Owerri, jihar Imo - Wani dalibin jami’ar fasaha ta tarayya da ke Owerri (FUTO) ya rasa ransa yayin da aka jikkata wasu da dama a wani lamari mai alaka da kungiyoyin asiri.

Kara karanta wannan
Rigima ta ƙara zafi a APC yayin da dakarun ƴan sanda suka ƙwace iko da sakateriya a jihar Arewa
Rahoton The Nation ya nuna cewa lamarin ya faru ne da safiyar ranar Jumu'a yayin da wasu ɗaliban jami'ar jihar Imo (IMSU) suka shiga harabar jami'ar FUTO.

Asali: Facebook
An tattaro cewa ɗaliban jami'ar IMSU sun shiga harabar gidan kwanan ɗalibai a FUTO a kan babura, lamarin da jawo suka yi arangama da juna.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A yayin faɗan da ya kaure tsakaninsu, daya daga cikin daliban jami'ar IMSU ya caka wa kwamandan tawagar Man O War na jami'ar FUTO wuƙa a wuya.
Wannan munanan raunuka da ya ji a wuyansa yayin rikicin ne ya zama ajalinsa, ya mutu nan take a wurin.
Mutuwar ɗalibin da kuma yadda aka ji wa wasu ɗalibai da dama raunuka ya jefa makarantar cikin yanayin jimami da kaɗuwa.
Matsalar tsaro a Kudu maso Gabas

Kara karanta wannan
Binance: Tsohon dan takarar shugaban kasa ya goyi bayan matakin da Shugaba Tinubu ya dauka
FUTO na daya daga cikin manyan jami'o'in gwamnatin tarayya a Najeriya da ke da matsuguni a Imo, ɗaya daga cikin jihohin Kudu maso Gabas, inda ake fama da matsalar tsaro.
A baya-bayan nan ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari tare da lalata kayayyakin kamfanin rarraba wutar lantarki na Najeriya (TCN) a jihar Imo. rahoton Guardian.
Yan sanda sun kama mahara 15
A wani rahoton kuma Ƴan sanda sun damƙe mutum 15 da ake zargin ƴan bindiga ne da masu hannu a aikata miyagun laifuka jihar Neja.
Kwamishinan ƴan sanda na jihar, Shawulu Ebenezer Danmamman, ya ce jami'an tsaron sun kuma kwato muggan makamai da alburusai.
Asali: Legit.ng