Mummunar Gobara Ta Lakume Shaguna Masu Yawan Gaske a Babbar Kasuwar Jihar Arewa, An Rasa Rai
- An samu tashin wata mummunar gobara a sashin yan kayan daki da ke babbar kasuwar Gusau, babban birnin jihar Zamfara
- Gobarar wacce ta tashi da misalin karfe 9:00 na dare ta janyo asarar dukiya mai tarin yawa bayan ta kona shaguna da dama
- Kwamandan hukumar kashe gobara ya tabbatar da afkuwar lamarin, ya ce wani mai shago ya rasa ransa a kokarinsa na kashe wutar ta karfi da yaji
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum
Jihar Zamfara - Rahotanni sun kawo cewa mummunar gobara ta lakume shaguna da dama a babbar kasuwar garin Gusau, babban birnin jihar Zamfara, inda aka kuma rasa rai daya.
An rahoto cewa gobarar ta tashi ne da misalin karfe 9:00 na daren ranar Talata, 30 ga watan Janairu, a sashin yan kayan daki da ke babbar kasuwar.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/16ec39c205a43237.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Jama'a sun shiga tashin hankali gobara ta kame wasu makarantun sakandare a Anambra
![Gobara ta lakume shaguna a babbar kasuwar Gusau Gobara ta lakume shaguna a babbar kasuwar Gusau](https://cdn.legit.ng/images/1120/2fefdb62e5c605d5.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Me hukumomi suka ce kan tashin gobarar?
Kwamandan hukumar kashe gobara ta Najeriya, ofishin sabuwar kasuwa, Hamza Mohammed, ya tabbatar da rasa ran mutum daya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya sanar da gidan talabijin na Channels cewa wani mai shago wanda har yanzu ba a bayyana sunansa ba ya mutu a lokacin da yake kokarin shiga shagonsa domin kashe gobara ta karfin tuwo.
Yan kwana-kwana daga hukumar jihar suna ta kokarin kashe gobarar tun daga karfe 9:00 na dare, don hana ta yaduwa zuwa sauran shaguna.
Mohammed ya bayyana cewa gobarar ta taba shaguna masu yawan gaske, amma har yanzu ba a san musabbbabin tashin ta ba, rahoton Naija News.
Gobara ta lakume miliyoyi a kasuwar waya
A wani labari makamancin wannan, mun ji a baya cewa shaguna da dama da dukiyoyi na miliyoyin Naira ne suka lalace a daren ranar Litinin bayan da gobara ta tashi a kasuwar waya ta Damaturu a jihar Yobe.
Jaridar Leadership ta tattaro cewa gobarar wacce ta tashi da misalin ƙarfe 6:23 na dare, ta ɗauki sa'o'i kafin a samu damar kashe ta.
Jami'an tsaro, ƴan kwana-kwana da jama'ar yankin ne dai suka yi haɗin gwiwa wajen kokarin ganin an kashe gobarar.
Asali: Legit.ng