Kungiyar Yarbawa ta Afenifere Ta Dauki Mataki Mai Tsauri Kan Shugabanta

Kungiyar Yarbawa ta Afenifere Ta Dauki Mataki Mai Tsauri Kan Shugabanta

  • An tsige Pa Ayo Adebanjo, mukaddashin shugaban kungiyar dattawan Yarbawa ta Afenifere daga kan kujerarsa
  • Afenifere ta tsige Adebanjo a matsayin shugabanta a taronta na wata wanda ya gudana a gidan Pa Reuben Fasoranti,jagoran kungiyar, a Akure, babban birnin jihar Ondo
  • Hakan na zuwa ne watanni bayan takaddamar da ta biyo bayan dan takarar da Adebanjo ya marawa baya sama da zabin mutane da yawa a kungiyar

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Akure, Ondo - Kungiyar dattawan Yarbawa ta Afenifere ta tsige Ayo Adebanjo a matsayin mukaddashin shugaban kungiyar.

An tsige Adebanjo ne a wajen taron wata na kungiyar wanda ya gudana a gidan jagoranta, Reuben Fasoranti, a Akure, babban birnin jihar Ondo.

Kara karanta wannan

Babu ruwanmu: Shugaban kungiyar Miyetti Allah bai hannunmu Inji Jami’an DSS

Kungiyar Afenifere ta tsige mukaddashin shugabanta
Kungiyar Yarbawa ta Afenifere Ta Dauki Mataki Mai Tsauri Kan Shugabanta Hoto: Afenifere
Asali: Twitter

Yadda aka tsige Adebanjo a matsayin shugaban Afenifere

Kamar yadda TVC ta rahoto, wani Farfesan tiyata Samuel Ibikunle mai ritaya ne ya gabatar da kudiri a kan haka, kuma Agboluaje daga jihar Oyo ya goyi bayansa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan ya biyo bayan shawarar da dattawan kungiyar ta Afenifere suka bayar.

Da yake yiwa manema labarai jawabi a karshen taron, kakakin kungiyar ta Afenifere, Jare Ajayi, ya ce an dauki matakin ne domin tabbatar da hadin kai da kuma magance rabuwa.

Ku tuna cewa alaka ta yi tsami tsakanin Adebanjo da Fasoranti, lamarin da ya sa shi fitowa ya yi bayanin cewa an nada tsohon shugaban jam'iyyar ne don ya yi riko a madadinsa saboda tsufa.

Yadda Adebanjo ya raba gari da Fasoranti a Afenifere

Rabuwar kan ya fara ne lokacin da Adebanjo ya lamuncewa Peter Obi, dan takarar jam'iyyar LP gabannin zaben ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.

Kara karanta wannan

2027: Tsohon hadimin Buhari ya bayyana abun da dinkewar Kwankwaso da Ganduje ke nufi ga PDP

A daya bangaren, tsagin Fasoranti sun lamuncewa Shugaban kasa Bola Tinubu, wanda shine dan takarar APC a zaben.

Tsagin Fasoranti ya yi bayanin cewa makasudin gina kungiyar shine daraja Bayarabe sama da komai. Don haka, suka ga ya cancanci su marawa Tinubu, Bayarabe baya, a matsayin dan takararta a zaben.

Rigingimun sun ci gaba har bayan zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu, kuma Tinubu ne ya lashe zaben.

FG ta karyata mayar da Legas babban birnin Najeriya

A wani labarin, Bayo Onanuga, mai ba shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu shawara ta musamman kan harkokin labarai ya yi watsi da rade-radin cewa Shugaban kasar na son mayar da babban birnin tarayyar kasar zuwa Legas.

Onanuga ya ce rade-radin mayar da babban birnin tarayyar kasar Legas ya fara ne a lokacin zaben shugaban kasa na 2023 daga bangaren abokan hamayyar Tinubu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng