Tsohon Gwamnan CBN Ya Ƙara Bankado Muhimmin Abu Kan Emefiele a Mulkin Buhari da Jonathan
- Tsohon gwamnan babban banki, Kingsley Moghalu, ya ayyana Godwin Emefiele a matsayin mafi munin gwamnan CBN a tarihin Najeriya
- A wani sako da ya wallafa a shafinsa ranar Asabar, 23 ga watan Disamba, Moghalu ya feɗe lokacin Emefiele a CBN
- Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya zargi tsoffin shugabanni biyu, Goodluck Jonathan da Muhammadu Buhari bisa aminta da shi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
FCT Abuja - Tsohon gwamnan babban bankin Najeriya CBN, Kingsley Moghalu, ya yi magana kan wa'adin da Godwin Emefiele ya shafe a matsayin gwamnan CBN.
Moghalu ya bayyana cewa, "babu tantama Emefiele shi ne gwamnan CBN mafi muni da cutarwa da aka taɓa yi a tarihin Najeriya."

Kara karanta wannan
"Ba Sabiu Tunde Yusuf Bane", Emefiele Ya Bayyana Wanda Ya Bada Umurnin Sauya Fasalin Naira

Asali: UGC
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, Mista Moghalu ya ce tsohon gwamnan CBN ɗin, "bai cancanta ba kuma bai shirya riƙe muƙamin ba ko kaɗan."
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Emefiele ya lalata komai a matsayin gwamnan CBN
Farfesan ya kuma bayyana cewa "daga dukkan bayanan da suka fito a yanzu," Emefiele ba shi da gaskiya.
Tsohon shugaban ƙasa, Dokta Goodluck Jonathan ne ya naɗa Emefiele, wanda ke matsayin manajan darakta a bankin Zenith, a matsayin gwamnan CBN a 2014.
Haka nan kuma tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, bayan ya karɓi mulki a 2015 ya ci gaba da aminta da tsohon ma'aikacin bankin.
Farfesa Moghalu ya ce:
"Zan faɗi ra'ayina game da abin da Emefiele ya yi a matsayin gwamnan CBN duk da wasu da ya kamata su yi faɗi hangensu sun yi shiru."

Kara karanta wannan
Alison Madueke ta roki Tinubu ya bari ta dawo Najeriya, ta tona asirin gwamnan PDP? Gaskiya ta fito
"Babu tantanma ko waswasi shi ne mafi muni wanda ya lalata komai a matsayin gwamnan CBN wanda ba a taɓa yin kamarsa ba a tarihin Najeriya."
"Bai cancanta ba kuma bai ma shirya riƙe mukamin ba kuma a iya bayanan da suka fito game da ayyukan da ya yi, babu shakka mutum ne mara gaskiya."
Jerin yan siyasar da aka ɗaure a 2023
A wani rahoton na daban kun ji cewa wasu ƴan siyasa masu faɗa a ji a Najeriya sun tsinci kansu a gidan gyaran hali saboda wasu dalilai.
Legit Hausa ta tattaro muku manyan ƴan siyasa biyu da kotu ta sa suka girbi laifukan da suka shuka a shekarar 2023 da ke dab da karewa.
Asali: Legit.ng