Akwai Alheri 1: Shugaba Tinubu Ya Gana da Shugaban UAE, Hotuna da Bayanai Sun Bayyana

Akwai Alheri 1: Shugaba Tinubu Ya Gana da Shugaban UAE, Hotuna da Bayanai Sun Bayyana

  • A wani gagarumin yunkuri kawo ci gaba, shugaba Tinubu ya gana da Sheikh Mohammed bin Zayed Al Nahyan, shugaban Hadaddiyar Daular Larabawa
  • Taron wanda aka gudanar a ranar Lahadi, 3 ga watan Disamba, an yi shi ne da nufin karfafa dankon zumunci tsakanin Najeriya da UAE
  • Tinubu ya bayyana irin nasarorin da aka samu a tattaunawar da suka yi tare da jaddada aniyarsu ta fadada alaka tsakanin kasashen biyu

Salisu Ibrahim kwararren editan fasaha, kudi da al'amuran yau da kullum ne, yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru takwas.

Dubai, UAE – Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata muhimmiyar ganawa da shugaban Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), Sheikh Mohammed bin Zayed Al Nahyan, a ranar Lahadi, 3 ga watan Disamba.

Shugaban ya bayyana haka ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X dauke da hotunan yadda ganawar ta kasance.

Kara karanta wannan

Tinubu ko Buhari: Bulaliyar Majalisa, Ndume, ya bayyana wanda ya fi, ya bai wa kowa maki

Shugaba Tinubu ya gana da shugaban UAE
Ganawar Tinubu da shugaban UAE | Hoto: @OfficialABAT
Asali: Twitter

Shugaba Tinubu ya wallafa cewa:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Mun yi wata ganawa mai muhimmanci da shugaban Hadaddiyar Daular Larabawa, Sheikh Mohammed bin Zayed Al Nahyan a yau, wanda zai karfafa alaka mai karfi tsakanin Najeriya da UAE da kuma kudurinmu na fadada alaka tsakanin kasashen biyu."

Su wa ke tare da Tinubu?

Kamar yadda aka gani a hotunan, Tinubu na tare da ma ba shi shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, da ministan ma'adanai, Dele Alake, da wasu manyan jami'an gwamnati.

Ganawar ta Lahadi ta zama ta biyu mafi muhimmanci da Shugaba Tinubu ya yi tun bayan da ya isa Dubai a wannan tafiyar.

Tun da farko, shugaban ya tashi daga Najeriya zuwa Hadaddiyar Daular Larabawa ne domin halartar taron kolin yanayi na COP28 da aka shirya gudanarwa a ranakun 1 da 2 ga watan Disamba, 2023, mai taken "Unite, Act, and Deliver".

Kara karanta wannan

Bai san ana yi ba, Sanatan APC ya fadi babban kuskuren Buhari a shekaru 8

Tinubu ya kinkimi mutane zuwa Dubai

A duk cikin kasashen Afrika da ke halartar taron COP28 da aka shirya a Dubai a kasar UAE, Najeriya ta fi kowa yawan tawaga.

Bayanan da aka samu daga hukumar UNFCCC ta majalisar dinkin duniya ya nuna Najeriya ta dauki mutum fiye da 1, 400 zuwa taron.

A duk Duniya, The Cable ta ce Najeriya ce ta uku – bayan kasar UAE inda ake taron sai kuma Brazil masu mutum 4,409 da 3,081.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.

Online view pixel