‘Haka Dama Najeriya Take’: Daga Dura Najeriya, Yaro Ya Firgita, Ya Shiga Mamaki

‘Haka Dama Najeriya Take’: Daga Dura Najeriya, Yaro Ya Firgita, Ya Shiga Mamaki

  • Wata mata ta nadi bidiyon yadda danta ya yi na ban dariya da ya ga dandazon jama'a a filin jirgin saman Najeriya a ziyararsa ta farko
  • Da yake bayyana rudani da firgici, ya yiwa mahaifiyarsa wata tambaya da ta baiwa ‘yan Najeriya da dama dariya
  • Jama’a da dama sun ga abin da ya faru, sun kuma bayyana ra'ayoyinsu a kafafen sada zumunta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wani karamin yaro ya kasa gaskata idanuwansa yayin da ya ga tulin mutane da yawa a filin jirgin saman Najeriya bayan ya isa kasar a ziyararsa ta farko.

Mahaifiyarsa ta bayyana cewa ziyararsa ta farko Najeriya kenan, inda ya kwashe da dariya har ya rude da ganin jama'a a filin jirgin.

Ta nadi abin da ya faru mai ban dariya yayin da suke tattaunawa. Cikin rudani a fuskarsa yaron ya kada baki yace, dama haka Najeriya take.

Kara karanta wannan

"Nuna mun alama": Budurwa ta ziyarci kabarin mahaifinta, ta nemi ya girgiza bishiya, bidiyon ya yadu

Yaro ya tsorata da shigowa Najeriya
Daga shiga Najeriya yaro ya firgita | Hoto: Maskot, Stringer
Asali: Getty Images

Matar dai ta bayyana mamakin yadda yaron ya ji, kana ta tsaya tunanin ya dan nata ke son ganin Najeriya idan ba haka ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bidiyon da aka yada a kafar TikTok ta hannun @stoner_012 ya jawo cece-kuce da yawa, ya kuma sa mutane suna ta magana.

Wasu kuwa, sun bayyana kadan daga abubuwan da zai ci karo dasu a matsayinsa na mai ziyara a kasa irin Najeriya.

Kalli bidiyon:

Martanin jama'a

@MummyJael :

"Ya kadu kuma abin da zai faru da 'ya'yana kenan saboda suna da buri da yawa! Kada dai a fada musu."

Daniel:

"Abin babu kyau dan yaro, kada ka damu za a fada ma Tinubu ya amince da ba da kyautar Kirsimeti."

ANUOLUWAPO OLUTOLA:

"Ku fada masa haka siddan ake dauke wuta ana kawowa. Kada ya fara kuka."

Kara karanta wannan

Matashi ya nuna yadda wayar iPhone dinsa ta makale a tukunya bayan ya yi kuskure wajen girki

yes_I'm_naveen:

"Watakila ya yi zaton mutane na rayuwa a cikin daji da bishiyoyi ne a Najeriya."

MBen:

"Shin babu mutane ne a jirgin da ya hau ya zo? Me yasa mutane za su bashi tsoro?"

Cynthia:

"A filin jirgnin sanda kake kuma har ka fara korafi ka bari ka shigo titi mana."

Budurwa ziyarci kabarin mahaifita

A wani labarin, wata matashiyar budurwa ta tsuma zukata a TikTok bayan ta yada wani bidiyo na ziyarar da ta kai kabarin mahaifinta.

Matashiyar mai suna @Iromicc a TikTok ta isa kabarin mahaifinta da ya rasu don yin magana da shi amma bata ji amsa daga gare shi ba.

A cikin bidiyo da ya yadu, ta roke shi da ya girgiza bishiya ko wani abu domin ta tabbatar da cewar yana sauraronta, amma babu abun da ya faru.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.