Ikon Allah: Yan Ta'adda Sun Mutu Yayin Da Bam Din Da Suka Dasa Ya Tashi Da Su a Jihar Borno

Ikon Allah: Yan Ta'adda Sun Mutu Yayin Da Bam Din Da Suka Dasa Ya Tashi Da Su a Jihar Borno

  • Mayakan kungiyar ISWAP huɗu sun sheka lahira yayin da bam ɗin da suka dasa ya tashi da su a jihar Borno
  • Rahotanni sun nuna cewa yan ta'addan sun ɗana bam ɗin a hanyar wucewar sojoji amma makircin ya ƙare a kansu ranar Laraba
  • Zagazola Makama ya tattaro cewa duk da ragargazar da aka yi musu, a yanzu yan ta'addan na neman dawo da tashin bama-bamai

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Borno - 'Yan ta'adda huɗu na ƙungiyar ISWAP sun mutu yayin da bam ɗin da suka dasa ya tashi da su a ƙauyen San San, karamar hukumar Mobbor ta jihar Borno.

Bam ya tashi da mayakan ISWAP a Borno.
Yan Ta'adda Sun Mutu Yayin da Bam Din da Suka Dasa Ya Tashi da Su a Jihar Borno Hoto: Borno State
Asali: UGC

Jaridar Leadership ta tattaro cewa mugun nufin yan ta'addan ya koma kansu sa'ilin da suka dasa bam a hanyar wucewar dakarun sojin birged ta 5 ranar Laraba da ta wuce.

Kara karanta wannan

Dubun wasu hatsabiban 'yan bindiga 8 da suka addabi mutane ya cika a jihar Kaduna

Bayanai sun nuna cewa bayan sun ɗana bam ɗin sai ya tashi da su, ya yi musu gunduwa-gunduwa a wurin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sojoji sun tono wani bam na daban

Bayan haka kuma, sojojin rundunar MNJTF na sashi na 4 da aka tura garin Chetima Wongonu sun tono wani bam da ake zargin yan ta'adda suka dasa a kusa da kauyen Chetimari.

Zagazola Makama, masani kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi ya ce yan ta'adda sun ƙara matsawa wajen amfani da ababen fashewa

A rahoton da ya wallafa a shafinsa na X, Makama ya ce:

"Gabanin faruwar lamarin, mayaƙan ISWAP sun buɗe wuta a Chetimari da daddare da nufin jawo hankalin dakarun sojoji saboda idan sun fito zasu taka bam ɗin."
"Duk da wannan makircin sojojin suka nuna turjiya kuma daga bisani suka gano abun fashewar da ƴan ta'addan suka dasa da misalin ƙarfe 6:30 na yamma, suka warware shi."

Kara karanta wannan

Wasu hadimai sun yi jabun sa hannun gwamnan APC don sace kuɗi? Gaskiya ta bayyana

Ya kuma tattaro cewa duk da yadda aka yi raga-raga da yan ta'adda tare da lalata musu kayan aiki da kashe wasu da dama, a yanzu suna neman komawa amfani da abubuwan fashewa.

Dubun masu garkuwa 8 ya cika a Kaduna

A wani rahoton na daban Yan sanda sun kama yan bindiga takwas da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a sassa daban-daban na jihar Kaduna.

Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan Kaduna, Mansir Hassan, ya faɗi sunayen waɗanda aka kama.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262