Yan bindiga Sun Shiga uku, Ɗan majalisar PDP Ya Bai Wa Jami'an Tsaro Kayan Aiki, Ya Tallafawa Mata

Yan bindiga Sun Shiga uku, Ɗan majalisar PDP Ya Bai Wa Jami'an Tsaro Kayan Aiki, Ya Tallafawa Mata

  • Honorabul Umar Yusuf yabo ya raba wa mutanen mazaɓarsa da hukumomin tsaro babura 200
  • Ɗan majalisar tarayyan ya kuma bai wa mata 2,000 jarin Naira N50,000 kana ya raba wa wasu matan firiza don su fara sana'a
  • Da yake jawabi, ya ce wannan somin taɓi ne kuma yana ɗaya daga cikin aƙawurran da ya ɗauka lokacin kamfe

Ahmad Yusuf, kwararren Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Sokoto - Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Yabo-Shagari, Umar Yusuf Yabo, ya bayar da tallafin babura 200 ga hukumomin tsaro da wasu mutane a mazaɓarsa.

Dan majalisar Yabo da Shagari, Yusuf Yabo ya raba wa mutanen mazaɓarsa kayan alheri.
Matsalar Tsaro: Dan Majalisar Sokoto Ya Raba Babura 200 Ga Hukumomin Tsaro Hoto: Ammar Muhammad Shagari
Asali: Facebook

Ya kuma baiwa mata 2,000 jari tare da gina famfunan ruwa 50 da kuma injinan samar da wutar lantarki mai karfin 2.5KVA guda 50 ga manoma da masallatai a yankunan biyu.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun buɗe wuta, sun yi garkuwa da shugabar ƙaramar hukuma a jihar Arewa

Bai tsaya iya nan ba, Dan majalisar ya kuma raba kayan makaranta 500 da litattafan rubutu 5,000 ga daliban firamare, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Da yake jawabi a wurin taron wanda ya gudana a garin Yabo ranar Litinin, Yusuf ya ce wannan tagomashin na cikin alkawuran da ya yi wa al’ummar mazabar a lokacin kamfe.

Ɗan majalisar ya ce:

"A lokacin yakin neman zabe, na yi wa al’ummarmu alkawarin kawo sauyi mai kyau domin Yabo/Shagari ta rasa wakilci na gari a zauren majalisar wakilai na tsawon shekaru da dama."
"Sabida haka abin da kuke gani yau ba komai bane illa mafarin kyawawan abubuwan da ke kan hanya."

Ya raba wa nata jarin N50,000

A cewarsa, kowacce daga cikin mata 2000 za ta samu tallafin Naira 50,000, inda ya kuma kara da cewa, akwai wasu mata 50 da za a ba su kyautar firiza kowace ɗaya.

Kara karanta wannan

'Dan Majalisar APC ya rantse da Allah, ya ce zasu tuhumi Tinubu kan yadda aka yi da kuɗin tallafin fetur

A rahoton The Sun, ya ci gaba da cewa:

"Na kuma miƙa koken matsalar wutar lantarki ga majalisa saboda yankunan Yabi da Shagari sun jima cikin duhu tsawon shekaru. Na muku alƙawarin hasken wutar lantarki zai dawo nan bada daɗewa ba."

Ijaw ta kudu ce zata raba gardama a Bayelsa

A wani rahoton na daban Ana hasashen ƙaramar hukuma ɗaya ce zata raba gardama a zaɓen Gwamnan jihar Bayelsa tsakanin APC da PDP.

Zuwa yanzun INEC ta karɓi sakamakon kananan hukumomi 7 kuma Gwamna Diri na PDP ne ke kan gaba da tazarar ƙuri'u 58,577.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262