Masarautar Bauchi Ta Tsige Masu Rike da Sarauta 6, Ta Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Hakimi

Masarautar Bauchi Ta Tsige Masu Rike da Sarauta 6, Ta Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Hakimi

  • Masarautar Bauchi ta tsige rawanin da aka naɗa wa sabbin masu riƙe da sarautar gargajiya shida a yankin Galambi
  • A wata sanarwa da masarautar da fitar, ta ce Hakimin Galambi ya saɓa wa doka da ƙa'idoji wajen naɗin sarauta
  • Ta kuma ɗauki matakin haramta wa hakimin naɗin sarauta na tsawon shekara ɗaya, wanda zai fara daga ranar 7 ga watan Nuwamba

Ahmad Yusuf, kwararren Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Bauchi - Majalisar Masarautar Bauchi ta tsige wasu sabbin masu rike da sarautar gargajiya guda shida a yankin Galambi da ke ƙarƙashin masarautar.

Masarautar Bauchi ta tsige rawanin mutane shida.
Masarautar Bauchi Ta Tuge Rawanin Sarautar da Aka Naɗa Wa Mutum Shida Hoto: Masoyan Sarkin Bauchi
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wannan matakin na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun Masarautar, Babangida Hassan Jahun, ya fitar.

Kara karanta wannan

To Fa: Ana jajibirin zaɓe, Ɗan takarar Gwamna na jam'iyyar APC ya sha da ƙyar, bayanai sun fito

Ya yi bayanin cewa an ɗauki wannan matakin ne bisa la'akari da matakan da hakimin Galambi, ya bi wajen naɗa wa mutanen Sarauta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar sanarwan, matakan da aka gano hakimin ya bi, sun saɓa wa doka da ƙa'idojin naɗin irin waɗannan Sarautar gargajiyan, kamar yadda Leadership ta ruwaito.

An tattaro cewa Hakimin, Alhaji Shehu Adamu Jumba wanda ke rike da sarautar Danlawal na Masarautar Bauchi, ya bai wa wasu mutane shida sarauta a fadarsa kwanakin baya.

Sarautar gargajiyar da ya naɗa wa mutanen su ne, Galadaman Danlawal, Wakilin Dokan Danlawal, Majidadin Danlawal, Wakilin Gonan Danlawal, Sarkin Dajin Danlawal da kuma Hardon Danlawal.

Masarautar Bauchi ta ɗauki mataki kan hakimin

Bugu da ƙari, Sanarwan ta kara da bayanin cewa Masarautar Bauchi ta haramta wa Hakimin yin kowane irin naɗin sarauta na tsawon shekara ɗaya wanda zai fara daga ranar 7 ga watan Nuwamba, 2023.

Kara karanta wannan

Dakarun sojin Najeriya sun halaka 'yan bindiga sama da 100, sun samu nasarori masu yawa

"Ya zama wajibi a ko da yaushe ya tabbatar da cewa duk wani mataki na naɗin Sarauta dole ne ya kasance ya yi daidai da doka da ka'idojin cikin masarautar," in ji sanarwan.

Ɗan majalisar LP ya yi nasara a Kotun ɗaukaka ƙara

A wani rahoton kuma Bayan Kotun zaɓe ta soke nasararsa, ɗan majalisar tarayya na LP daga Legas ya samu nasara a Kotun ɗaukaka ƙara.

Kotun ta jingine hukuncin farko, kana ta tabbatar da Thaddeus Attah a matsayin sahihin ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Eti Osa a Legas.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262