Ba Shi da Son Duniya, Bagudu Ya Fadi Inda Tinubu Ya Ke Kwana Kafin Zama Shugaban Kasa

Ba Shi da Son Duniya, Bagudu Ya Fadi Inda Tinubu Ya Ke Kwana Kafin Zama Shugaban Kasa

  • Yayin da ake ci gaba da cece-kuce kan siyan jirgin ruwan alfarma na Tinubu, Minista Bagudu ya kare shugaban
  • Ministan Kasafi da Tsare-tsare ya ce Shugaba Tinubu mutum ne mai kan-kan da kai wanda bai damu da abin duniya ba
  • Bagudu ya bayyana haka ne a jiya Juma'a 3 ga watan Nuwamba yayin taron kara wa juna sani na ministoci a Abuja

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Ministan Kasafi da Tsare-tsare a najeriya, Atiku Bagudu ya bayyana Shugaba Bola Tinubu a matsayin mutum mai kan-kan da kai.

Bagudu ya bayyana haka ne a jiya Juma'a 3 ga watan Nuwamba a Abuja yayin taron kara wa juna sani na ministoci na kwanaki uku.

Kara karanta wannan

Gwamnan PDP da kujerarsa ke tangal-tangal ya nemi afuwar talakawan jiharsa kan abu 1 da ya faru

Bagudu ya kare Tinubu kan zargin siyan jirgin ruwan alfarma
Bagudu ya yi martani mai zafi kan zargin siyan jirgin ruwan Tinubu. Hoto: Bola Tinubu, Atiki Bagudu.
Asali: Facebook

Mene Bagudu ke cewa kan Tinubu?

Ministan na magana yayin kare shugaban kan cece-kuce da ake yi na siyan jirgin ruwan alfarma da ake zargin shugaban da yi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce wannan jirgin ruwan da ake magana ba an siyo shi ba ne don amfanin shugaban kasar, cewar Daily Trust.

Ya ce:

"Wannan rashin fahimta da aka yi na jirgin sojin ruwan ya jawo kace-nace a kasar.
"Amma idan har a kasafin tiriliyan 2.2, kaso 95 ba wani matsala, ina tunanin ya kamata a yaba wa Shugaba Tinubu a kan haka."

Wane yabo Bagudu ya yi wa Tinubu?

Ya kara da cewa shugaban ba shi da wata bukata ta kayatarwa na jrigin ruwa, abin da ya cimma a rayuwarsa ya ishe shi, cewar Trust Radio.

Ya kara da cewa:

"Kafin ya zama shugaban kasa, ya na kwana ne a gida mai dakuna uku kacal a Abuja, ya na rayuwa cikin kan-kan da kai ba tare da son duniya ba."

Kara karanta wannan

‘'Gwamnatin Tinubu za ta tsamo 'yan Najeriya miliyan 50 daga kangin talauci,’' Betta Edu

Tinubu ya yi martani kan zargin siyan jirgin ruwa

A wani labarin, Shugaba Bola Tinubu ya yi martani kan cece-kucen da ake yi cewa ya siya jirgin ruwan alfarma na makudan kudade.

Shugaban ya ce ba shi da abin da zai yi da wannan jirgin inda ya ce tsohuwar gwamnatin Buhari ce ta siye shi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.