EFCC: Mutane Sun Yi Zanga-Zanga a Majalisa Saboda Nadin Shugaban da Aka Yi

EFCC: Mutane Sun Yi Zanga-Zanga a Majalisa Saboda Nadin Shugaban da Aka Yi

  • Kungiyar Centre for Democracy & Human Rights (CEDEHUR) ta na yaki da nada Olu Olukoyede ya zama shugaban hukumar EFCC
  • Sakataren wannan kungiya mai zaman kan ta ya fadawa majalisar dattawa cewa tantance wanda aka turo zai zama sabawa doka
  • Kwamred Adebayo Ogorry ya hakikance cewa doka ba ta ba Ola Olukoyede damar rike EFCC ba domin ba jami’in ‘dan sanda ba ne

Abuja - A daidai lokacin da majalisar dattawa ta ke shirin tantance wadanda za su shugabanci EFCC, sai aka ji wasu su na adawa da hakan.

Business Day ta ce an wasu ba su goyon bayan Ola Olukoyede da Muhammad Hammajoda su jagoranci hukumar yaki da rashin gaskiyar.

Wata kungiya mai suna 'Centre for Democracy and Human Rights' da mutanenta sun fito karara, su na adawa da nadin Olu Olukoyede a EFCC.

Kara karanta wannan

Ba Tinubu Ya Ci Zabe Ba – Sakataren Gwamnatin Buhari Ya Fadi Asalin Wanda Ya Yi Galaba

EFCC.
Sababbin shugabannin EFCC Hoto: @officialEFCC
Asali: Twitter

"Za a sabawa dokokin EFCC" - CEDEHUR

‘Yan kungiyar sun gudanar da zanga-zanga, su na zargin an sabawa doka wajen nada wanda zai canji Abdulrasheed Bawa a hukumar ta EFCC.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sakataren kungiyar na kasa, Kwamred Adebayo Ogorry yake cewa abin da Bola Ahmed Tinubu ya yi, ya ci karo da rantsuwar karbar mulki.

Adebayo Ogorry ya na ganin idan nadin ya tabbata, an yi wa dokoki hawan kawara.

Shugabancin EFCC sai 'Dan sanda

Ikirarin da jagoran na kungiyar CEDEHUR ya ke yi shi ne zaman lauyan shugaban EFCC zai ci karo da sashe na dokar da ta kafa Hukumar.

Da yake fassara dokar, Ogorry ya ce EFCC ba ta fararen hula ba ce, don haka ake bukatar wanda zai zama shugabanta ya kasance ‘dan sanda.

Idan aka tabbatar da tsohon sakataren, CEDEHUR ta na ganin an bude kofar saba doka. Zargin da fadar shugaban kasa ta musanya tuni.

Kara karanta wannan

Yanzu Nan: Kotu ta Tsige Sanatan Adamawa, ‘Dan Takaran PDP Ya Samu Nasara

"Aikin Shugaban kasa Bola Tinubu wajen nada Mr Olukoyede a babban ofis mai dauke da nauyi sosai na shugaban EFCC ya ci karo da tanadin dokokin majalisa kuma ya sabawa rantsuwar da ya yi a ranar 29 ga watan Mayun 2023, na cewa zai kare dokokin kasar nan."

- Adebayo Ogorry

Rahoton da ya fito dazu kuwa shi ne Majalisar dattawa za ta tantance sabon shugaban hukumar EFCC yau Laraba duk da surutun jama’a.

Tantancewar na zuwa ne bayan Bola Tinubu ya nemi majalisar ta amince da naɗin da ya yi, wanda ya jawo abin magana ta fuskar dokar kasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng