Daga Karshe, An Gano Shugaban Fulani da Ya Bata a A Jihar Filato a Mace

Daga Karshe, An Gano Shugaban Fulani da Ya Bata a A Jihar Filato a Mace

  • Dakarun soji sun gano gawar shugaban Fulanin da ya ɓata tun watan Satumba a jihar Filato da ke Arewa ta Tsakiya
  • Shugaban MACBAN reshen jihar da rundunar Operation Save Haven sun tabbatar da gano gawar Ardo Adamu Idris
  • A ranar 24 ga watan Satumba, 2023 aka ayyana ɓatan Arɗo kuma COAS ya umarci Sojoji su nemo shi duk inda ya ke

Plateau - An gano gawar Arɗo, shugaban Fulani na gundumar Panyam a karamar hukumar Mangu da ke jihar Filato, Adamu Idris, wanda ya ɓata a kwanakin baya.

Shugaban kungiyar Fulani Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) reshen jihar Filato, Nuru Abdullahi, shi ne ya tabbatar da gano gawar.

An gano gawar shugaban Fulanin da ya ɓata.
Daga Karshe, An Gano Shugaban Fulani da Ya Bata a A Jihar Filato a Mace Hoto: dailytrust
Asali: UGC

Ya bayyana cewa za a masa jana'iza kamar yadda addini ya tanada a jihar Bauchi da ke Arewa maso Gabashin Najeriya, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Kano: Duk da Kotu Ta Tsige Shi, Abba Gida-Gida Ya Bada Hutun Kwana Ɗaya Na Murnar Haihuwar Annabi SAW

Shugaban kungiyar ta MACBAN ya ce an gano gawar Arɗon ne a ƙauyen Dawaki da ke yankin ƙaramar hukumar Kanke a jihar Filato.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke wanzar da zaman lafiya a yakin jihar Filato, Captain Oya James, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Yadda Ardo Idris ya ɓace a watan Satumba

Idan baku manta ba, babban hafsan rundunar sojin ƙasa ta Najeriya, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ya bada umarnin gaggauta nemo gawar shugaban Fulanin a ko ina take.

A ranar 27 ga watan Satumba, 2023, Shugaban hukumar sojin ya bai wa dakarun sojin rundunar Operation Save Haven umarnin zaƙulo gawar mutumin cikin awanni 24 kaɗai.

Kwana biyu gabanin haka watau ranar 25 ga watan Satumba, aka bayyana cewa Arɗo Adamu Idris, ya ɓata ba a san inda ya shiga ba domin bai koma gida ba.

Kara karanta wannan

Sanatoci Sun Tsige Shugaban Majalisar Dattawa Daga Muƙaminsa Kan Abu 1? Gaskiya Ta Bayyana

An tattaro cewa shugaban Fulanin ya bata ne a daidai lokacin da yake kan hanyar koma wa gida bayan ya ziyarci hakimin yankin, Aminu Darwam, Daily Post ta ruwaito.

Mohbad: Primeboy Ya Mika Kansa Ga Yan Sanda Bayan Ayyana Nemansa Ruwa a Jallo

A wani rahoton kuma Primeboy, abokin fitaccen mawaƙin nan da ya mutu Mohbad ya miƙa kansa ga rundunar yan sandan jihar Legas.

Wannan na zuwa ne bayan rundunar 'yan sanda ta ayyana nemansa ruwa a jallo kuma ta sanya ladan Naira miliyan ɗaya ga duk wanda ya taimaka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262