Shettima Ya Jagorancin Taron NEC a Fadar Shugaban Kasa Da Ke Abuja

Shettima Ya Jagorancin Taron NEC a Fadar Shugaban Kasa Da Ke Abuja

  • Mataimakin shugaban ƙasa, Ƙashim Shettima, na jagorantar taron majalisar NEC yanzu haka a Aso Villa da ke Abuja
  • Rahoto ya nuna gwamnonin jihohi da dama sun halarci taron na yau Alhamis karo na uku bayan rantsar da shugaban ƙasa, Bola Tinubu
  • Wannam taro na zuwa ne kwanaki ƙalilan bayan kungiyoyin ma'aikatan Najeriya sun ayyana shiga yajin aikin sai baba ta gani daga 3 ga watan Oktoba

FCT Abuja - Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, na jagorantar taron majalisar ƙoli ta tattalin arzikin Najeriya (NEC) a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

The Nation ta tattaro cewa yanzu haka Shettima na jan ragamar taron NEC na wannan watan kuma karo na uku tun bayan rantsar da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima.
Shettima Ya Jagorancin Taron NEC a Fadar Shugaban Kasa Da Ke Abuja Hoto: Kashim Shettima
Asali: Facebook

Gwamnonin jihohin da suka halarci taron

Gwamnonin jihohin da aka hanga sun halarci taron sun haɗa da, Osun, Legas, Kaduna, Adamawa, Ribas, Benuwe, Sokoto, Delta, Ebonyi, Taraba, da kuma Nasarawa.

Kara karanta wannan

"Ba Zamu Yi Murnar Ranar Samun 'Yancin Kai Ba" Gwamnan APC a Arewa Ya Bayyana Dalilai

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Haka nan kuma Ministan babban birnin tarayya Abuja kuma tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya halarci taron da dai sauran mambobin NEC, kamar yadda daily trust ta ruwaito.

Wannan taro na yau Alhamis na zuwa ne kwanaki ƙalilan bayan ƙungiyoyin kwadago sun ayyana shirinsu na tsayar da harkoki cak gaba ɗaya ranar 3 ga watan Oktoba.

Ƙungiyoyin kwadagon sun ayyana shiga yajin aiƙin sai baba ta gani ne bisa abin da suka kira gazawar gwamnati na samar wa 'yan Najeriya mafita biyo bayan wahalhalun cire tallafin fetur.

A taron karshe ranar 17 ga watan Agusta, NEC ta amince da ware zunzurutun kudi har Naira biliyan 5 ga kowace jiha daga jihohi 36 da birnin tarayya Abuja.

Majalisa ta ɗauki matakin ne domin a siyo kayan abinci da takin zamani a wani bangare na kokarin rage radadin da aka shiga sakamakon cire tallafin man fetur a kasar nan.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: 'Yan Ta'adda Sun Sake Kai Ƙazamin Hari Jihar Kaduna, Sun Halaka Mutane da Yawa

Kotun Zaɓe Ta Yanke Hukuncin Kan Nasarar Wani Gwamma

A wani rahoton kuma An tabbatar da Fasto Umo Eno na jihar Akwa Ibom a matsayin sahihin wanda ya lashe zaɓen gwamna ranar 18 ga watan Maris, 2023.

Kotun zaɓe mai zama a Uyo, babban birnin jihar ta kori kararrakin jam'iyyun ADC da NNPP da 'yan takararsu bisa hujjar rashin cancanta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel