Matsalar Tsaro: Abinda Ya Sa Iyaye Ke Fargabar Tura 'Ya'yansu Makaranta, Ministan Tinubu

Matsalar Tsaro: Abinda Ya Sa Iyaye Ke Fargabar Tura 'Ya'yansu Makaranta, Ministan Tinubu

  • Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa iyaye na tsoron tura 'ya'yansu makaranta ne saboda tsoron harin yan bindiga
  • Ministan harkokin cikin gida, Tunji-Ojo ya ce yawan hare-haren da ake kaiwa makarantu tun 2014 babban abin damuwa ne
  • Gwamnan jihar Benuwai ta tabbatar da cewa gwamnatinsa zata bada goyon baya a shirin samar da aminci a makarantun jihar

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

FCT Abuja - Ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ya ce a yanzu iyaye na tsoron tura 'ya'yansu makaranta saboda matsalar tsaron da ta damu ƙasar nan.

Tunji-Ojo ya faɗi haka ne a sakonsa na fatan alheri da ya gabatar a wajen taron kaddamar da tsarin “Samar da tsaro a makarantu” da aka gudanar a Makurdi, babban birnin jihar Benuwai.

Ministan cikin gida, Tunji-Ojo.
Matsalar Tsaro: Abinda Ya Sa Iyaye Ke Fargabar Tura 'Ya'yansu Makaranta, Ministan Tinubu Hoto: dailytrust
Source: UGC

Ya ce, "Iyaye suna tsoron tura 'ya'yansu makaranta saboda tsoron kai hare-haren 'yan ta'adda."

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu Ya Gana da Gwamnan PDP Da Tawagar Masu Ruwa da Tsakin Jiharsa a Villa

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa Ministan ya yi jawabi ne ta bakin kwamandan rundunar jami'an Sibil Difens (NSCDC), Ahmed Abubakar Audi, wanda ya wakilce shi a wurin taron.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ministan ya jaddada cewa taɓarɓarewar tsaro da yawan kai hari makarantun ƙasar nan tun 2014 irin wanda aka sace ɗaruruwan ɗalibai mata a Chibok, ba ƙaramin abun damuwa bane.

Sai dai a nasa jawabin a wurin bikin yaye jami'ai 364 da aka ba horon samar da tsaro a makarantun Benuwai da sauran jihohi, Mista Audi ya yaba da tsarin tsaro a makarantu.

Wane nasarori sabon tsarin tabbatar da tsaro a makarantun ya samu?

Ya bayyana cewa zuwa yanzu shirin ya daƙile kai hare-hare sama da 30 a makarantun fadin kasar, tun bayan da aka fara aiwatar da shi a Najeriya, rahoton Trust Radio.

Gwamna Hyacinth Alia, a jawabinsa na musamman a wajen bikin, ya yi alkawarin goyon baya daga gwamnatinsa wajen ba da fifiko kan harkokin tsaro a makarantu, inda ya jaddada muhimmiyar rawar da ilimi ke takawa wajen ci gaba.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tarayya Ta Ba Mambobin Majalisar Wakilai Tallafin N100m? Gaskiya Ta Fito Filii

Shugaba Tinubu Ya Sa Labule da Ganduje da Hafsoshin Tsaro a Villa

A wani rahoton kuma Bola Ahmed Tinubu ya gana da shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, da manyan hafsoshin tsaro a Aso Villa.

Wakilan ƙungiyar fulani makiyaya ta ƙasa MACBAN sun halarci zaman wanda ya maida hankali kan muhimmin batu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262