Shugaba Tinubu Ya Turawa Jihar Ogun Buhunan Shinkafa 3,000 a Matsayin Rage Radadin Cire Tallafin Man Fetur

Shugaba Tinubu Ya Turawa Jihar Ogun Buhunan Shinkafa 3,000 a Matsayin Rage Radadin Cire Tallafin Man Fetur

  • Tuni gwamnatin jihar Ogun ta fara tsara yadda da ta yi rabon kayayyakin abinci ga marasa galibi
  • Gwamnatin Tarayya ta umarci a ba jihohi kudade domin siya wa talakawa kayan abinci a shekarar nan
  • Tun bayan cire tallafin man fetur ake fama da matsanancin fatara a Najeriya saboda haihuwar farashin kayayyaki

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Ogun - Gwamnatin jihar Ogun ta karbi buhunan shinkafa guda 3,000 na farko daga gwamnatin tarayya domin cika alkadarin shirinta na raba abinci ga ‘yan Najeriya domin rage tasirin cire tallafin man fetur, The Nation ta ruwaito.

Sakataren gwamnatin jihar Ogun, Mista Olatokunbo Talabi, wanda ya tabbatar da hakan a ranar Juma’a yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai, ya ce za a fara rabon shinkafar ne bayan an kammala shirin rabon.

Kara karanta wannan

Babbar Sarki Ya Najeriya Ya Tunatar da Tinubu, Ya Faɗi Hanya 1 da Za a Karya Farashin Man Fetur

Talabi ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta karbo kudi daga gwamnatin tarayya domin siyan hatsi a wani bangare na kudin da aka tsara na siyan kayayyakin abinci da kowace jiha za ta rabawa mazaunanta.

Tinubu ya aika kayan abinci zuwa Ogun
Yadda za a fara rabon kayan abinci a Ogun | Hoto: @OfficialABAT
Asali: Twitter

Gwamnatin jihar Ogun za ta yi karin tallafi

Sakataren ya yi nuni da cewa, gwamnatin jihar na kara sayo hatsi don karawa kan wanda gwamnatin tarayya ta bayar domin isar mazauna jihar, rahoton Daily Post.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

A cewarsa, za a fara mai da hankali ga marasa galihu da kuma nasassu da mata a wannan rabon kayayyakin abinci da za a yi nan kusa.

Ya ce:

“Za a ba da kulawa ta musamman ga tsofaffi, nakasassu, da mata, da sauransu, wajen rabon kayayyakin.”

Ya kara da cewa tuni gwamnatin jihar ta kafa kwamitin mutane masu kishin da za su ruwa su yi tsaki wajen tabbatar da rabon kayan tallafin.

Kara karanta wannan

Shugaban 'Yan Bindiga Ya Ayyana Kansa a Matsayin Gwamnan Jihar Arewa? Gaskiya Ta Bayyana

Akwai yiwuwar a dawo da tallafin man fetur

A wani labarin, Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya na tunanin fito da wani tsarin wucin gadi na tallafin man fetur lura da halin da ake ciki.

A sakamakon yadda farashin gangar mai da kudin kasar waje su ka tashi, The Cable ta ce Mai girma Bola Ahmed Tinubu zai iya lashe amansa.

Fadar shugaban kasa ba ta yanke matsaya ba tukuna, amma an bijiro da wannan magana kuma watakila shugaban kasar ya amshi shawarar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.